Toggle menu
24K
663
183
158.1K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

UMD NFLC Hausa Lessons/132 Relief Organizations Expelled From Darfur

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
(Redirected from UMD NFLC Hausa Lessons/132)


Overview

Lesson Title: Relief Organizations Expelled From Darfur

This is an interview with a doctor about relief agencies in Darfur.

  1. Language: Hausa
  2. Topic: Economics/Politics
  3. ILR Level: 2+/3
  4. ACTFL Proficiency: Superior, Advanced-High
  5. This ACTFL rating is an approximation based on the ILR level
  6. Modality: Listening
  7. Learning Objective: Maintenance & Improvement
  8. Subject Area: Language
  9. Material Type: LLO
  10. Publication Year: 2009
  11. ObjectID: T8LHA09

Transcript


Source Text Translation
A: To kwanakin baya gwamnati Sudan ta ba da sanarwar korar kungiyoyin agaji na kasashen waje daga yankin Darfur, ta kuma kwace dukkan kadarorin su, a bayan da kotun duniya ta tuhumi Shugaba Albashir da aikata laifukan yaki. To, na tambayi Dr.Yusuf Lawan Gusau, na Hukumar Kula da Yawan Jama’a ta Majalisar Dinkin Duniya wanda yake aiki a yankin na Darfur, ko ta yaya wannan kora ta shafi ayyukansu na tallafawa ’yan gudun hijira da suke Darfur?

B: Alhaji Ibrahim gaskiya wannan lamari ya taba mu ya girgiza mu kuma sosai, saboda a zaman da ake ciki yanzu akwai kungiyoyi wato {international non-governmental organizations [ English] } da kuma NOHA duk kungiyoyi masu zaman kansu na kasa da kasa guda goma sha hudu wa’yanda aka kora da kuma ’yan kasa guda biyu. Idan ka hada ke nan an samu kungiyoyi goma sha shidda . {Now [ English]} kungiyoyin nan goma sha shida akalla suna taimaka ma mutum miliyan hudu da dubu dari bakwai, na daya ke nan. Na biyu idan ka dubi ma’aikatansu ma kwata-kwata, ma’aikatan wadanda aka kora na wa’yannan kungiyoyi sun kai dubu shidda da dari biyar -

A:– Ma’aikata kawai ke nan na -

B:– Ma’aikata kawai na wa’yanan kungiyoyi da aka kora - -

A: - Haka

B: uma an ba su umarni ne na tattara an yi girshi an anshe musu kaddarori kamar motoci kamar kwamfutoci da kuma duk wasu kayayyaki na sadarwa an karbe. Wani lokutan ma idan ka je banki amsar kudi, sai a ce maka babu kudi a ciki. Sannan wa’yannan kungiyoyin kuma Alhaji Ibrahim, inda sunka taba mu, misali ka ga, ni a ofishina na san da muna da asibitoci wadanda muke kula da shiyu kusan talatin da wani abu a yankin gaba dai. Wa’yannan kungiyoyi su suka taimaka suka kirkiro wadannan asibitoci, wadannan kungiyoyi su suka taimaka suka nemo malaman aiki, masu aiki kamar likitoci da nas hakan nan, sannan su ke taimakawa wajen biyan albashin su, sannan idan aka samu mara lahiya, ba ta da lafiya kuma su ke sai mata magani kyauta,ah na daya ke nan. Na biyu akwai wata kungiyar ka ga kamar misali a yanzu {WAP, Wood-All Food Programme [English]} ah suna taimakawa ne wajen ciyar da ainihin su ’yan sansanin gudun hijira kamar wadanda yaki ya ci, {IDC [English]} ke nan.

A: ’Yan gudun hijira na cikin gida.

B: ’Yan gudun hijira na cikin gida! Suna taimaka masu suna ci she su da abinci, saboda su mata ke zuwa neman abinci, namiji da ka hita waje idan {rebel [ English]} suka gan ka su kashe. To, gudun a kaucewa wannan lamari, sai su {World Food Programme [ English]} suke rarrabawa wa’yannan mutane abinci, to amman da ka’ida ta Majalisar Dinkin Duniya, mu {agencies [English]} ba ma aiki {directly [English]} mu je mu yi wannan aiki, sai dai mu nemi {NGOs [ English]} mu ba su wannan aiki su je su yi, to yanzu an wayi gari an ce wanda ke ba ka abinci an kore shi, wanda ke ba ka magani an kore shi, wanda ke ba ka ruwan sha an kore shi, to yaya matsayin rayuwarka ke nan? Ka ga abubuwa za su sake muni ke nan wanda za a koma ’yar gidan jiya.

A: Dr.Yusuf korar wadannan kungiyoyin da aka yi idan har ta zauna, tana nufin cewa ke nan ku ma ayyukan da kuke gudanarwa a matsayinku na jami’an Majalisar Dinkin Duniya a wannan yanki na Darfur zai kare ko yaya?

B: A, a, ba zai kare ba, za mu ci gaba, illa dai an han- tagayyara mu, ba mu san yadda za mu yi {filling [ English]} wannan {gap [ English]} din ba, saboda wadanda muke aiki da su an riga an kore su, ka ga dole yanzu mu koma {drawing board [English]} mu samo hanyoyin da ya kamata mu bi domin mu cim ma wadannan mutanen kar su shiga halin{ ha’ula’I [ Arabic]}. Yau, yanzu hakan nan ina can Khartum, mun zo mun yi {meeting [ English]} yadda za a yi a yi {filling [English]} wannan {gap [ English]} din, muna nan muna roko ga {Arab League [ English]} da {African Union [ English]} a su yi kokari don Allah su cim ma shi {Mr. President [ English]} ya dan tausaya wadannan mutane a maishe da su. Ko da an riga an yi muni, an riga an bata abubuwa, saboda akasarinsu duk sun bar kasar.

The Government of Sudan Orders the United Nation Relief Agencies Out of the Darfur Region

A: Well, recently, the government of Sudan made an announcement that they were expelling international aid organizations from the Darfur region and also seizing all of their assets, after the International Court accused President al-Bashir of committing war crimes. So, I asked Dr. Yusuf Lawan Gusau, who works in the Darfur region with the United Nations Population Fund, how this expulsion has affected their refugee assistance activities in Darfur.

B: Alhaji Ibrahim, this situation has certainly affected us. We are very shocked by it because currently there are 14 groups, that is, international nongovernmental organizations and NOHA [unknown acronym]—all independent international organizations that have been expelled—along with two domestic groups. That makes 16 organizations all together. Now, first of all, these 16 organizations have been providing aid to at least 4,700,000 people. That’s the first thing. Secondly, if you consider the total number of workers, the personnel from these expelled organizations, that would be about 6,500—

A: That’s just the number of personnel—

B: —just the personnel from these organizations that were expelled.

A: I see. . .

B: And they were ordered to come together and take an inventory of their equipment, like vehicles, computers, and any other communications gear, and this equipment was confiscated. Sometimes you go to the bank to withdraw money, but you are told that there’s isn't money. And [what happened to] these organizations [has] affected us, Alhaji Ibrahim. For example, you see, in my office, I know that we have nearly 30 clinics that we oversee in the conflict zone. These organizations are the ones that helped set up these clinics. These organizations helped find staff, like doctors and nurses, and they’ve also been helping to pay their salaries. And when people are sick, if someone is sick, they are the ones who provide that person with free medicine. That’s the first thing. Secondly, there are organizations, you see, like the WAP, the World-All Food Programme [error in source text; this should be WFP, World Food Programme], that, um . . . that help provide food for people living in refugee camps who can't feed themselves . . . that is, IDPs.

A: Internally Displaced Persons . . . ?

B: Yes, Internally Displaced Persons! [These organizations] help them by providing them with food. It’s the women who come in search of food, because if the men go out and the rebels see them, they will kill them. So they flee, and the WFP people distribute food to these people. But according to United Nations regulations, our agencies can’t go out and do this work directly. We find NGOs [nongovernmental organizations] and give them the task of going out and doing this work. So, now you wake up and are told that the people who were providing you with food have been expelled; the people who were providing you with medicine have been expelled; the people who were providing you with drinking water have been expelled. So, what is your life like then? You see, the situation is going to deteriorate, and this is a big step backwards.

A: Dr. Yusuf, if the expulsion of these organizations holds, does it mean that the activities you oversee in your position as United Nations officials in the Darfur region will come to an end?

B: No, they won’t end; we will keep going. It’s just that we are suffering, and we don’t know how we’re going to go about filling this gap, because the people we have been working with have already been expelled. So, you see, now we have to go back to the drawing board and find ways of reaching these people to prevent further suffering. Earlier today I was in Khartoum, where we just had a meeting on how to go about filling this gap, and we were there pleading with the Arab League and the African Union to try, for God's sake, to convince Mr. President to have a little compassion towards these people and let them return. But the damage has already been done because the majority of them [the organizations] have left the country.

Glossary

Items Explanations
kayayaken sadarwa telecommunication equipment
Majalisar Ɗinkin Duniya United Nations
tagayyaramu to bring suffering
halin hawala'i hardship, difficult situation
an wayi gari an (lit: wake up and become aware of the world around) apprehend, realize, discover
mkasarinsu majority of them
a koma 'yar gidan jiya (lit: to return to yesterday's) to experience a repetition of past events

Notes

1. Darfur Conflict

According to “War in Darfur” from Wikipedia, the conflict began in early 2003 when the Sudan Liberation Army took up arms against the Arab-dominated central government of Sudan, accusing it of discrimination. Many of the atrocities in the war have been blamed on the Janjaweed, the militia of Arab nomads allied with the government. The UN has estimated that 400,000 people have died and that 2 million have been displaced since the war began. In March 4, 2009, the International Criminal Court in Hague issued an arrest warrant for Sudanese president Omar al-Bashir over alleged war crimes committed in the western region of Darfur.

War in Darfur. (2009, May 29). Wikipedia. Retrieved May 29, 2009, from http://en.wikipedia.org/wiki/War_in_Darfur

2. Aid to Darfur

Despite the significant safety and security issues, many international relief organizations operate in the Darfur region to provide assistance to the victims of the humanitarian crisis. Their presence is vital to the people of Darfur, but many of them have been forced by the government to suspend their operations. Some organizations have also been looted or their office buildings have been burned. Jan Egeland, UN under-secretary general for humanitarian affairs, while reporting on an incident of blankets being stolen, said, “There seems to be a deliberate attempt to inject suffering on the civilian population.”

4 million people in Darfur now need humanitarian aid, top UN relief official says. (2006, November 20). UN News Center. Retrieved May 29, 2009, from http://www.un.org/apps/news/story.asp?NewsID=20658&Cr=sudan&Cr1

3. More Information

For a list of current relief organizations operating in Sudan, consult the following link:

http://www.interaction.org/sudan/