Toggle menu
24.1K
670
183
158.6K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir2: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Line 689: Line 689:


=== Tafsiri: ===
=== Tafsiri: ===
A cikin wadannan ayoyi Allah swt yana bayyana cewa, shi kadai ne mai mulkin sammai da qasa da abin da yake cikinsu, kuma shi ne mai cikakken iko a kan komai. Sannan ya sanar da cewa, a cikin halittar sammai da qasa da abubuwan da suka qunsa da cancanzawar dare da rana, wannan ya zo, wannan ya tafi, lalle akwai manya-manyan ayoyi da dalilai ga masu lafiyayyen hankali, da suke tabbatar da samuwar Mahalicci da siffofinsa.
A cikin wadannan ayoyi Allah swt yana bayyana cewa, shi kadai ne mai mulkin sammai da qasa da abin da yake cikinsu, kuma shi ne mai cikakken iko a kan komai. Sannan ya sanar da cewa, a cikin halittar sammai da qasa da abubuwan da suka qunsa da cancanzawar dare da rana, wannan ya zo, wannan ya tafi, lalle akwai manya-manyan ayoyi da dalilai ga masu lafiyayyen hankali, da suke tabbatar da samuwar Mahalicci da siffofinsa. Wadannan kuwa su ne masu ambaton Allah koyaushe, a cikin kowane yanayi, a tsaye suke ko a zaune ko a kwance. Suna tunani game da halittar sammai da qasa, suna cewa: "Ya Ubangijinmu, mun yi imani ba ka yi wannan halittar a banza ba; ka tsarkaka daga yin wannan, don haka ka tsare mu daga da shi, kuma azzalumai ba su da masu taimaka musu." Suka ci gaba da cewa: "Ya Ubangijinmu, mun ji Annabinka yana kira zuwa ga yin imani da kai, kuma mun amsa kiransa, mun yi imani, don haka ka gafarta mana laifukanmu, kuma ka kankare mana munanan ayyukanmu, kuma ka karb'i rayukanmu tare da mutanen kirki. Ya kyakkyawan sakamako ka zartar da shi, kada kuma ka kunyata mu a ranar alqiyama a gaban halittunka; lalle mun tabbatar ba ka sab'a alqawari."


pg487
Sai ko Allah swt ya bayyana cewa, ya karb'i wannan roqo nasu, kuma ya yi alqawarin ba zai tab'a tozarta aikin mai aiki ba, namiji ne shi ko mace ce. Don haka wadanda suka baro garuruwansu na kafirci ko kuma kafirai suka koro su, aka cutar da su saboda sun riqe gaskiya, sun yi imani da Allah da Manzonsa, suka kuma yi yaqi don Allah, kuma aka kashe su, to wadannan Allah zai kankare musu laifukansu, kuma zai saka su gidajen Aljanna, wadanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu; wannan babban sakamako ne a gare su, saboda qoqarin da suka yi na aikin alheri a duniya. Allah shi ne mai kyakkyawan sakamako ga duk wanda ya yi aikin qwarai; zai saka masa da abin da ido bai tab'a gani ba, kunne bai tab'a ji ba, zuciyar wani d'an Adam ba ta tab'a tunaninsa ba.
 
An karbo daga Abdullahi d'an Abbas rA ya ce: Wani dare na kwana a d'akin Maimuna uwar muminai. kuma a ranar Annabi SAW yana d'akinta, domin in ga yadda yake sallarsa ta dare. Annabi SAW ya yi hira da iyalinsa na wani d'an lokaci, sannan ya kwanta ya yi barci. A sulusin qarshe na dare, sai ya tashi zaune, ya d'aga kai sama, sai ya karanta wannan aya (ta Quran/3/190), sannan ya tashi ya yi alwala, ya yi asiwaki, sannan ya yi salla raka'a goma sha d'aya, sannan Bilal ya kira sallar Asuba. Sai Annabi SAW ya sallaci raka'a biyu, sannan ya fita ya jagoranci sallar Asuba. [Bukhari #7452].
 
Narrated Ibn `Abbas: Once I stayed overnight at the house of (my aunt ) Maimuna while the Prophet (ﷺ) was with her, to see how was the night prayer of Allah's Apostle Allah's Messenger (ﷺ) talked to his wife for a while and then slept. When it was the last third of the night (or part of it), the Prophet (ﷺ) got up and looked towards the sky and recited the Verse:-- 'Verily! In the creation of the Heavens and the Earth....there are indeed signs for the men of understanding.' (3.190) Then He got up and performed the ablution, brushed his teeth and offered eleven rak`at. Then Bilal pronounced the Adhan whereupon the Prophet (ﷺ) offered a two-rak`at (Sunna) prayer and went out to lead the people in Fajr (morning compulsory congregational prayer. https://sunnah.com/bukhari:7452
 
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:'''
# Kira zuwa ga yin tunani game da halittar sammai da qasa, saboda abubuwan da suka qunsa na manyan dalilai masu tabbatar da Ɗayantakar Allah da cancantar a bauta masa shi kad'ai.
#
 
pg488
[[Category:Quran/3]]
[[Category:Quran/3]]