Toggle menu
24.2K
670
183
158.8K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/18/IRIB Hausa Tafsir: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
No edit summary
Line 862: Line 862:
=== Suratul Kahfi, Aya Ta 95-101 (Kashi Na 517) ===
=== Suratul Kahfi, Aya Ta 95-101 (Kashi Na 517) ===
Jama'a masu saurare Asslamu alaikum barkanmu da sake saduwa da ku a cikin wannan shiri na hannuka mai sanda, inda muke yin dubi a cikin ayoyin kur'ani mai tsarki, tare da yin bayani gwargawdon iko kan abin da suke koyar da mu, tare da yi mana hannunka mai sanda a cikin lamurran rayuwa. Har yanzu muna cikin surat kahfi, sai a biyo mu sannu a hankali a cikin shirin.
Jama'a masu saurare Asslamu alaikum barkanmu da sake saduwa da ku a cikin wannan shiri na hannuka mai sanda, inda muke yin dubi a cikin ayoyin kur'ani mai tsarki, tare da yin bayani gwargawdon iko kan abin da suke koyar da mu, tare da yi mana hannunka mai sanda a cikin lamurran rayuwa. Har yanzu muna cikin surat kahfi, sai a biyo mu sannu a hankali a cikin shirin.
Sai a saurari karatun ayoyi na (95) da (96) a cikin surat Kahfi
Sai a saurari karatun ayoyi na (95) da (96) a cikin surat Kahfi
قَالَ مَا مَكَّنِّي فِيهِ رَبِّي خَيْرٌ فَأَعِينُونِي بِقُوَّةٍ أَجْعَلْ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ رَدْماً{95} آتُونِي زُبَرَ الْحَدِيدِ حَتَّى إِذَا سَاوَى بَيْنَ الصَّدَفَيْنِ قَالَ انفُخُوا حَتَّى إِذَا جَعَلَهُ نَاراً قَالَ آتُونِي أُفْرِغْ عَلَيْهِ قِطْراً{96}
قَالَ مَا مَكَّنِّي فِيهِ رَبِّي خَيْرٌ فَأَعِينُونِي بِقُوَّةٍ أَجْعَلْ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ رَدْماً{95} آتُونِي زُبَرَ الْحَدِيدِ حَتَّى إِذَا سَاوَى بَيْنَ الصَّدَفَيْنِ قَالَ انفُخُوا حَتَّى إِذَا جَعَلَهُ نَاراً قَالَ آتُونِي أُفْرِغْ عَلَيْهِ قِطْراً{96}
95 - Ya ce: "Abin da Ubangijĩna Ya mallaka mini, a cikinsa yã fi zama alhẽri. Sai ku taimake ni da karfi, in sanya babbar katanga a tsakãninku da tsakãninsu."
95 - Ya ce: "Abin da Ubangijĩna Ya mallaka mini, a cikinsa yã fi zama alhẽri. Sai ku taimake ni da karfi, in sanya babbar katanga a tsakãninku da tsakãninsu."
96 - "Ku kãwo mini guntãyen bakin karfe". har a lõkacin da ya daidaita a tsakãnin duwãtsun biyu (ya sanya wutã a cikin karfen) ya ce: "Ku hũra (da zugãzugai)." Har a lõkacin da ya mayar da shi wutã, ya ce: "Ku kãwo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa."
96 - "Ku kãwo mini guntãyen bakin karfe". har a lõkacin da ya daidaita a tsakãnin duwãtsun biyu (ya sanya wutã a cikin karfen) ya ce: "Ku hũra (da zugãzugai)." Har a lõkacin da ya mayar da shi wutã, ya ce: "Ku kãwo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa."
A cikin shirin da ya gabata an yi bayani kan wasu mutane da Zulkarnain ya samu suna rayuwa a tsakanin wasu manyan tsaunuka biyu, wadanda suke fuskantar barazanar tsaro daga wasu muggan mutane azzalumai da suke cutar da su, sai suka nemi taimakon Zulkarnai kan ya gina musu wata katanga da za ta raba tsakaninsu wa wadannan jama’a masu shishigi, a kan za su ba shi ladar wannan aiki.
A cikin shirin da ya gabata an yi bayani kan wasu mutane da Zulkarnain ya samu suna rayuwa a tsakanin wasu manyan tsaunuka biyu, wadanda suke fuskantar barazanar tsaro daga wasu muggan mutane azzalumai da suke cutar da su, sai suka nemi taimakon Zulkarnai kan ya gina musu wata katanga da za ta raba tsakaninsu wa wadannan jama’a masu shishigi, a kan za su ba shi ladar wannan aiki.
Sai Zulkarnain ya ce musu zai yi musu wannan aiki, amma su taimaka masa da karfafa daga cikinsu, su dauko masa karafa da zai yi wannan aiki da su, kuma suka yi aiki kamar yadda ya bukace su har ya kammala gina musu katangar karfe da ta kange su daga yajuju da majuju, sai ya ce musu abin da ya yi mani na falala ya fi abin da kuke son saka mini da shi na lada.
Sai Zulkarnain ya ce musu zai yi musu wannan aiki, amma su taimaka masa da karfafa daga cikinsu, su dauko masa karafa da zai yi wannan aiki da su, kuma suka yi aiki kamar yadda ya bukace su har ya kammala gina musu katangar karfe da ta kange su daga yajuju da majuju, sai ya ce musu abin da ya yi mani na falala ya fi abin da kuke son saka mini da shi na lada.
Darussan da za a dauka a nan su ne :
Darussan da za a dauka a nan su ne :
1 – Waliyan Allah suna shiga gaba-gaba wajen taimakon mabukata da warware matsalolinsu gwargwadon ikon da Allah ya ba su.
1 – Waliyan Allah suna shiga gaba-gaba wajen taimakon mabukata da warware matsalolinsu gwargwadon ikon da Allah ya ba su.
2 – Haduwar mutane a kan aiki na jama’a domin ci gabansu ta fuskar rayuwarsu ta zamantakewa ko tsaro ko tattalin arziki, shi ne babban mabudin nasararsu.
2 – Haduwar mutane a kan aiki na jama’a domin ci gabansu ta fuskar rayuwarsu ta zamantakewa ko tsaro ko tattalin arziki, shi ne babban mabudin nasararsu.
3 – Ko da mutane suna da abin da za su biya kansu bukata na daga kudade ko kayan aiki, amma kuma ba su da sahihin jagoranci da zai nuna musu hanya, to za su wanzu cikin fangima ne, domin Zulkarnaini ya sami mutane da duka bin da suke bukata domin su kare kansu daga yajuju da majuju, amma babu wanda ya san yadda za a yi hakan a cikin sai da Zulkarnaini ya sa musu hannu.
3 – Ko da mutane suna da abin da za su biya kansu bukata na daga kudade ko kayan aiki, amma kuma ba su da sahihin jagoranci da zai nuna musu hanya, to za su wanzu cikin fangima ne, domin Zulkarnaini ya sami mutane da duka bin da suke bukata domin su kare kansu daga yajuju da majuju, amma babu wanda ya san yadda za a yi hakan a cikin sai da Zulkarnaini ya sa musu hannu.
Sai a saurari karatun ayoyi na (97) da (98) a cikin surat Kahfi
Sai a saurari karatun ayoyi na (97) da (98) a cikin surat Kahfi
فَمَا اسْطَاعُوا أَن يَظْهَرُوهُ وَمَا اسْتَطَاعُوا لَهُ نَقْباً{97} قَالَ هَذَا رَحْمَةٌ مِّن رَّبِّي فَإِذَا جَاء وَعْدُ رَبِّي جَعَلَهُ دَكَّاء وَكَانَ وَعْدُ رَبِّي حَقّاً{98}
فَمَا اسْطَاعُوا أَن يَظْهَرُوهُ وَمَا اسْتَطَاعُوا لَهُ نَقْباً{97} قَالَ هَذَا رَحْمَةٌ مِّن رَّبِّي فَإِذَا جَاء وَعْدُ رَبِّي جَعَلَهُ دَكَّاء وَكَانَ وَعْدُ رَبِّي حَقّاً{98}
97 - Dõmin haka bã za su iya hawansa ba, kuma bã zã su iya huda shi ba.
97 - Dõmin haka bã za su iya hawansa ba, kuma bã zã su iya huda shi ba.
98 - Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijĩna. Sai idan wa'adin Ubangijĩna ya zo, ya mayar da shi nikakke. Kuma wa'adin Ubangijĩna ya kasance tabbatacce."
98 - Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijĩna. Sai idan wa'adin Ubangijĩna ya zo, ya mayar da shi nikakke. Kuma wa'adin Ubangijĩna ya kasance tabbatacce."
Wannan ayar tana yin ishara da abubuwan muhimmai guda uku, na daya : katangar da Zulkarnain ya gina tana tsawo da gwabi, kuma ta ginu matukar ginuwa, ta yadda yajuju da majuju ba za su iya haurawa kanta ba ko huda ta.
Wannan ayar tana yin ishara da abubuwan muhimmai guda uku, na daya : katangar da Zulkarnain ya gina tana tsawo da gwabi, kuma ta ginu matukar ginuwa, ta yadda yajuju da majuju ba za su iya haurawa kanta ba ko huda ta.
Abu na biyu shi ne : Zulkarnain bai danganta wannan aiki da kansa ba ko mutanen da suka taimaka masa, ya danganta hakan da rahamar ubangiji ga mutanen wannan wuri domin tsaronsu da kuma zaman lafiyarsu.
Abu na biyu shi ne : Zulkarnain bai danganta wannan aiki da kansa ba ko mutanen da suka taimaka masa, ya danganta hakan da rahamar ubangiji ga mutanen wannan wuri domin tsaronsu da kuma zaman lafiyarsu.
Abu na uku shi ne : Ya isar musu da sako cewa akwai wata rana da za ta zo wato kiyama, wadda alkawalin ubangijin dukkanin talikai ce, idan wannan rana ta zo to komai na duniya zai rushe ita ma wannan katangar duk da kwarinta za ta rushe ta warwartse saboda tsananin girgizar da kasa za ta yi a wannan rana, kuma zuwan wannan babu tantama a cikinsa, domin kuwa Alkawalin ubangiji ne, kuma alkawalin ubangiji gaskiya ne.
Abu na uku shi ne : Ya isar musu da sako cewa akwai wata rana da za ta zo wato kiyama, wadda alkawalin ubangijin dukkanin talikai ce, idan wannan rana ta zo to komai na duniya zai rushe ita ma wannan katangar duk da kwarinta za ta rushe ta warwartse saboda tsananin girgizar da kasa za ta yi a wannan rana, kuma zuwan wannan babu tantama a cikinsa, domin kuwa Alkawalin ubangiji ne, kuma alkawalin ubangiji gaskiya ne.
Darussan da za a dauka a nan su ne :
Darussan da za a dauka a nan su ne :
1 – Yin aiki tare da dikka da kuma kyautata shi na daga abin da aka sani a cikin sira ta waliyyan Allah, abin buga misali da shi kan hakan ita ce katangar Zulkarnain, wadda aka gina dubban shekaru, kuma tana ci gaba da wanzuwa har ranar tashin kiyama.
1 – Yin aiki tare da dikka da kuma kyautata shi na daga abin da aka sani a cikin sira ta waliyyan Allah, abin buga misali da shi kan hakan ita ce katangar Zulkarnain, wadda aka gina dubban shekaru, kuma tana ci gaba da wanzuwa har ranar tashin kiyama.
2 – Bayin Allah na gari a koda yaushe suna danganta duk wata fala da suka samu a rayuwarsu zuwa ga Allah, domin kuwa sun san cewa Allah shi ne mai kowa da komai.
2 – Bayin Allah na gari a koda yaushe suna danganta duk wata fala da suka samu a rayuwarsu zuwa ga Allah, domin kuwa sun san cewa Allah shi ne mai kowa da komai.
3 – Duk nasarar da muka samu a cikin kowane irin lamari na duniya, to kada kuma mu manta da kiyama ranar da komai zai kare sai mulkin Allah.
3 – Duk nasarar da muka samu a cikin kowane irin lamari na duniya, to kada kuma mu manta da kiyama ranar da komai zai kare sai mulkin Allah.
Sai a saurari karatun ayoyi na (99) zuwa (101) a cikin surat Kahfi
Sai a saurari karatun ayoyi na (99) zuwa (101) a cikin surat Kahfi
وَتَرَكْنَا بَعْضَهُمْ يَوْمَئِذٍ يَمُوجُ فِي بَعْضٍ وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَجَمَعْنَاهُمْ جَمْعاً{99} وَعَرَضْنَا جَهَنَّمَ يَوْمَئِذٍ لِّلْكَافِرِينَ عَرْضاً{100} الَّذِينَ كَانَتْ أَعْيُنُهُمْ فِي غِطَاء عَن ذِكْرِي وَكَانُوا لَا يَسْتَطِيعُونَ سَمْعاً{101}
وَتَرَكْنَا بَعْضَهُمْ يَوْمَئِذٍ يَمُوجُ فِي بَعْضٍ وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَجَمَعْنَاهُمْ جَمْعاً{99} وَعَرَضْنَا جَهَنَّمَ يَوْمَئِذٍ لِّلْكَافِرِينَ عَرْضاً{100} الَّذِينَ كَانَتْ أَعْيُنُهُمْ فِي غِطَاء عَن ذِكْرِي وَكَانُوا لَا يَسْتَطِيعُونَ سَمْعاً{101}
99 - Kuma Muka bar sãshensu a rãnar nan yanã garwaya a cikin sãshe, kuma aka bũsa a cikin kaho sai muka tãra su, tãrãwa.
99 - Kuma Muka bar sãshensu a rãnar nan yanã garwaya a cikin sãshe, kuma aka bũsa a cikin kaho sai muka tãra su, tãrãwa.
100 - Kuma Muka gitta Jahannama, a rãnar nan ga kãfirai gittãwa.
100 - Kuma Muka gitta Jahannama, a rãnar nan ga kãfirai gittãwa.
101 - Wadanda idãnunsu suka kasance a cikin rufi daga tunãni, kuma sun kasance bã su iya saurãrãwa.
101 - Wadanda idãnunsu suka kasance a cikin rufi daga tunãni, kuma sun kasance bã su iya saurãrãwa.
Idan muka kwatanta wannan aya da abin daka ambata acikin aya ta 96 a cikin surat Anbiya, za a iya fahimtar cewa a lokacin tashin kiyama ya zo katangar Zulkarnain za ta rushe, kuma yajuju da majuju za su sake afklawa kan mutane suna masu kai mummnan hari, tare da figita mutane da watsa su, za su kame wasu bangarori a kan doron kasa, daga karshe kuma mutane za su bar duniya baki daya bayan busa kaho, a lokacin busa kaho na biyu duk su hallara a wurin da za a yi tashin kiyama, a lokacin wadanda suka kafirce ma Allah a rayuwar duniya, suka yi sharholiya suka sheke aya, za su kuka su yi da sun sani a lokacin da Allah ya bijiro da wutar jahannama, domin su sun kasance suna kawar da kansu daga sakon Allah ba su su ma sauraren abin da ake gaya musu na daga ayoyin Allah, a ranar kiyama babu aiki balantana mutum ya yi istigfari, ko kuma ya yi wani aikin ibada domin ya samu lada.
Idan muka kwatanta wannan aya da abin daka ambata acikin aya ta 96 a cikin surat Anbiya, za a iya fahimtar cewa a lokacin tashin kiyama ya zo katangar Zulkarnain za ta rushe, kuma yajuju da majuju za su sake afklawa kan mutane suna masu kai mummnan hari, tare da figita mutane da watsa su, za su kame wasu bangarori a kan doron kasa, daga karshe kuma mutane za su bar duniya baki daya bayan busa kaho, a lokacin busa kaho na biyu duk su hallara a wurin da za a yi tashin kiyama, a lokacin wadanda suka kafirce ma Allah a rayuwar duniya, suka yi sharholiya suka sheke aya, za su kuka su yi da sun sani a lokacin da Allah ya bijiro da wutar jahannama, domin su sun kasance suna kawar da kansu daga sakon Allah ba su su ma sauraren abin da ake gaya musu na daga ayoyin Allah, a ranar kiyama babu aiki balantana mutum ya yi istigfari, ko kuma ya yi wani aikin ibada domin ya samu lada.
Darussan da za a iya dauka a nan su ne :
Darussan da za a iya dauka a nan su ne :
1 – Daga cikin alamun karshen duniya, mutane za su rude su yi ta fangima, wasu masu mugunta kuma za su yi ta cutar da sauran raunana.
1 – Daga cikin alamun karshen duniya, mutane za su rude su yi ta fangima, wasu masu mugunta kuma za su yi ta cutar da sauran raunana.
2 – Da dama daga ni’imomin duniya hanyoyi ne tuna Allah da gode masa, amma mafi yawan mutane ba su tuna Allah a lokacin da suke cikin ni’ima da walwala.
2 – Da dama daga ni’imomin duniya hanyoyi ne tuna Allah da gode masa, amma mafi yawan mutane ba su tuna Allah a lokacin da suke cikin ni’ima da walwala.
Da wannan ne muka kawo karshen shirin namu na wannan lokaci, sai idan Allah ya kai mu a shiri na gaba za mu ci gaba daga inda muka tsaya, amma kafin wannan lokacin, a madadin wadanda suka hada mana sautin shirin, nake yi muku fatan alkhairi, sai saduwa ta gaba, wassalamu alaikum wa rahmatullah wa barakatuh.
Da wannan ne muka kawo karshen shirin namu na wannan lokaci, sai idan Allah ya kai mu a shiri na gaba za mu ci gaba daga inda muka tsaya, amma kafin wannan lokacin, a madadin wadanda suka hada mana sautin shirin, nake yi muku fatan alkhairi, sai saduwa ta gaba, wassalamu alaikum wa rahmatullah wa barakatuh.