Toggle menu
24.2K
670
183
158.7K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

fatiha: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
No edit summary
Line 67: Line 67:
In-book reference: Book 4, Hadith 41
In-book reference: Book 4, Hadith 41


HUKUNCIN KARATUN FATIHA A CIKIN SALLAH 3.
@ Ba aya ba ce a fatiha, sa’annan kuma ba komai bace a cikin Surorin Kur’ani.
Wannan it ace fahimtar Mazhabar Malikiyyah.
Dalilin su itace kamar haka:
• Hadisin Aisha (RA) ta ke cewa: “MANZON ALLAH SAW YA KASANCE YANA BUDE SALLAH DA KABBARA, DA KARANTA ALHAMDULILLAH RABBIL ALAMIN”
Imam Muslim ya Ruwaito shi a Babin Sallah 1/357 Hadisi mai lamba 498.
• Hadisin Anas (RA) yake cewa: “ NA YI SALLAH A BAYAN ANNABI SAW, DA ABUBAKAR DA UMAR DA USMAN, AMMA SUN KASANCE SUNA BUDE SALLAH DA ALHAMDULILLAH RABBIL ALAMIN”.
Bukhari 2/188, Muslim 1/299, Abu Dauda a Hadisu mai lamba 782, Tirmizy a Hadisi mai lamba 246.
A wata riwayar da Imam Muslim ya ruwaito daga Anas (RA) yace “SUN KASANCE (Wato Manzon Allah SAW, Abubakar, Umar, da Usman) BA SA AMBATON [BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM] A FARKON KARATO KO A KARSHEN SA”.
• Daga cikin dalilan su na cewar Bismillah ba aya ba ce a fatiha, Hadisin Abu Hurairah (RA) yace: Na ji Manzon Allah SAW yana cewa: Allah Madaukakin Sarki yace: “NA RABA SALLAH TSAKANI NA DA BAWA NA GIDA BIYU, KUMA  BAWA NA YANA DA ABUN DA YA TAMBAYA.
IDAN BAWA YA CE: ALHAMDULILLAH RABBIL ALAMIN.
SAI ALLAH SWA YACE : BAWA NA YA GODE MUN.
IDAN BAWA YA CE: ARRAHMANIR RAHIM.
SAI ALLAH SWA YACE: BAWA NA YA YABE NI………………”
Sai su ka ce: Fadin Allah ‘NA RABA SALLAH” yana nufin Fatiha, ya sanya mata sunan Sallah, domin Sallah bata inganta sai da ita, da ace Basmalah aya ce a fatiha da an aambace ta a cikin wannan Hadisin na Kudsi.
• Da ace Basmalah aya ce a fatiha da zai zama akwai Maimaicin [ARRAHMANIR RAHIM], sai ya zama Surar da zama kamar haka [بسم اللرحمن الرحيم, الحمد لله رب العالمين, الرحمن الرحيم] wannan sai ya zama kamar  babu tsare na Balagha a kai. Kamar yadda suka fada.
• Su ka ce rubuta ta a farkon surori anyi ne don tabarraki da ita (ma’ana don a bambance tsakanin sura da sura), rubuta ta a farkon surori ba yana nufin ita ma aya ce a kur’ani ba.
Ibnul Arabi Almaliki yace: WANNAN ZAI NUNA MAKA CEWAR BA AYA BACE A KUR’ANI SABAODA SABANIN MUTANE AKAN TA, ALKUR’ANI KUMA BABU SABANI A CIKIN SA, BAYANAI SAHIHAI SUN NUNA [BASMALAH] BA AYA BA CE A FATIHA KO WANINTA, SAI DAI A CIKIN SURATUL NAMLI (Kamar yadda na bayyana hakan a baya).
Ya ci gaba da cewa: LALLAI MAZHABAR MU [Malikiyyah] SUN RINJAYAR DA HAKA KO DA TA HANYAR HANKALI NE, WANNAN YASA  TUN  ZAMANIN MANZON ALLAH SAW, HAR ZUWA LOKACIN IMAM MALIK, A MASALLACIN ANNABI SAW DAKE MADINA, BABU WANI DA YA TABA KARANTA [بسم الرحمن الرحيم] A CIKIN SALLAH, SABODA KOYI DA SUNNAH…..”
Don Karin bayani duba Tafsirin Qurdabi 1/93 da Ahkamul Kur’an na Ibnul Arabi 1/20.
@ Aya ce a Fatiha da ko wace Surah.
Wannan itace fahimtar Mazhabar Shafi’iyyah.
KU BIYO NI SANNU A HANKALI INSHA ALLAHU.
Muhammad Albani Misau
16/2/2016.
[[Category:Hadiths]]
[[Category:Hadiths]]
[[Category:Quran]]
[[Category:Quran]]
[[Category:Quran/1]]
[[Category:Quran/1]]