Toggle menu
24.1K
669
183
158.4K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir2: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Line 630: Line 630:
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:'''
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:'''
# Kwadaitarwa a kan yawaita aikata ayyukan alheri kafin zuwan ajali, saboda babu wanda ya san lokacin mutuwarsa.
# Kwadaitarwa a kan yawaita aikata ayyukan alheri kafin zuwan ajali, saboda babu wanda ya san lokacin mutuwarsa.
#
#Nuna kaskancin duniya da rashin tabbas dinta, domin duk wani abin jin dadi da yake cikinta mai gushewa ne. Don haka bai kamata ta rudi mai hankali ba.
#Ya kamata mumini ya sani cewa, duk irin yanayin da yake ciki, mai dadi ko marar dadi, wata jarrabawa ce daga Allah, domin ya ga godiyarsa ko hakurinsa, ko kuma rashinsu.
#Allah ya ba muminai labarin abin da za su rika gani daga magabtansu, Ma'abota Littafi da mushirikai, na cutarwa mai yawa, domin wasu hikimomi kamar haka:
##Don a tantance Musulmi na kwarai da lalatacce.
##Don Allah ya daukaka darajar muminai da wannan ya kuma kankare musu laifuffukansu.
##Don imaninsu ya ƙaru yayin da suka ga aukuwar abin da Allah ya ba su labarinsa.
##Don su shirya wa faruwar hakan.
##Don idan ya faru su yi hakuri, su jure.


pg481
== 187-188 ==
 
# Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya dauki alkawari daga wadanda aka bai wa Littafi cewa: "Lalle ku bayyana shi ga mutane, kuma kada ku boye shi." Sai suka jefar da shi can bayansu, kuma suka musanya shi da wani dan farashi kankani. To tir da abin da suke yin musanye da shi. --[[Quran/3/187]]
# Kada ka yi tsammanin wadanda suke yin farin ciki da irin abin da suka aikata, kuma suna son a rika yabon su da abin da ba su aikata ba, to kada ka yi tsammanin za su tsira daga azaba, kuma suna da azaba mai raɗaɗi. --[[Quran/3/188]]
 
Tafsiri:
 
A wadannan ayoyi, Allah swt yana tuna wa Annabinsa SAW wani mummunan aiki na Yahudawa da Nasara, lokacin da Allah ya yi ƙaƙƙarfan alkawari da su na cewa, za su fito su bayyana wa mutane abin da yake cikin littattafan da aka saukar wa annabawansu, kuma ba za su boye komai daga ciki ba. Daga ciki kuwa har da siffofin Annabi SAW da suka zo a Attaura da Linjila; to amma sai suka saɓa wannan alƙawari, suka ɓoye waɗannan siffofin Annabi SAW, ba don komai ba, sai don ɗan abin da za su samu na duniya. Sai Allah ya yi tir da irin wannan aiki nasu.
 
An karbo daga Abu Huraira rA ya ce: Annabi SAW ya ce: "Duk wanda aka yi masa tambaya ta ilimi, sannan ya boye, to za a sa masa linzamin wuta ranar gobe qiyama." [Abu Dawud #3658 da Tirmizi #2649 da ibnu Majah #266].
 
Narrated Abu Hurairah: that the Messenger of Allah (ﷺ) said: "Whoever is asked about some knowledge that he knows, then he [[conceals]] it, he will be bridled with bridle of fire." [https://sunnah.com/tirmidhi:2649<nowiki>]</nowiki>
 
pg484
[[Category:Quran/3]]
[[Category:Quran/3]]