Toggle menu
24.1K
669
183
158.4K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir2

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Revision as of 01:35, 16 May 2024 by Admin (talk | contribs)

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 100-101 na Surar Ali Imran

  1. Ya ku wadanda suka yi imani, idan kuka bi wani bangare na wadanda aka ba wa Littafi, to za su mayar da ku kafirai bayan imaninku. --Quran/3/100
  2. Ta yaya kuma za ku kafirce, ga shi kuwa ana karanta muku ayoyin Allah, kuma Manzonsa yana tare da ku? Duk kuwa wanda ya riki Allah, to hakika an shiryar da shi tafarki madaidaici. --Quran/3/101

A wadannan ayoyi Allah yana gargadin muminai da cewa, idan suka kuskura suka nuna biyayyarsu ga Yahudawa da Nasara, wadanda suke yi musu hassadar Alqur'ani da Allah ya ba su da falalar Musulunci; to tabbas za su raba su da imaninsu, su mayar da su kafirai suna ji suna gani. Amma Allah ya nuna cewa, da wahala kwarai muminai su yarda su koma kafirci bayan ga Alkur'ani nan kullum suna ji ana karanta musu ayoyinsa, sannan ga Manzon Allah nan a tsakaninsu, yana isar musu duk wani saƙo da aka saukar dominsu. Shi imani idan har ya ratsa ƙoƙon zuciya; to abu ne mai wuyar gaske a iya cire shi, sai dai wani iko na Allah.

Sannan Allah ya bayyana musu wata hanya wadda idan suka bi ta, za su tsare kawunansu daga fadawa ramin kafirci. Wannan hanya ita ce, rike Allah da dogaro da shi, domin shi ne madogara ta samun shiriya. Duk wanda ya koma ga Allah a cikin kowanne hali nasa, ya nemi mafaka a wurinsa, ya dogara da shi dogaro na gaskiya, ya rike addininsa; to hakika wannan an shiryar da shi ga hanya mikakkiya dodar, wadda babu karkata ko kadan a cikinta, ita ce za ta yi masa jagoranci har ta kai shi gidan Aljanna.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Gargadin Musulmi a kan su yi hattara wajen yarda da maganganun Yahudawa da Nasara da aiki da su, ko kwaikwayon wani tsari nasu na rayuwa, domin zukatansu cike suke da hassada da kullata ga Musulmi, a kullum suna tunanin hanyar da za su bi su raba Musulmi suka yi sakaci suka karbi tsare-tsarensu na rayuwa; to za su iya kai su ga halaka.
  2. Sanin falalar