(41 intermediate revisions by the same user not shown) | |||
Line 1: | Line 1: | ||
[[Quran/3]] > [[Quran/3/Rijayar_Lemo_Tafsir]] > [[Quran/3/Rijayar_Lemo_Tafsir2]] | |||
== Ma'arif Al-Qur'an tafsir of verses 3:1 to 3:4 [https://quran.com/3:2/tafsirs/en-tafsir-maarif-ul-quran] == | |||
The first verse of this section presents a rational proof of the Oneness of Allah (don nuna babu mai iya kawo kamarsa); the second verse, the reported proof 1, followed by an answer to some doubts nursed by disbelievers towards the later part. | |||
1. In the terminology of Islamic theology, a proof based on rational argument is called rational proof while a proof based on a verse of divine book or on a declaration made by an authority or a report narrated by a trustworthy person is called a reported proof. | |||
The first word, Alif Lam Mim (الم ) at the head of the first verse be-longs to the special set of words used by the Qur'an ([[mu'ujizar]] Alƙur'ani) which are words of hidden meaning and are known as Mutashabihat متشبھات ، the real meaning of which is a secret between Allah and His Messenger ﷺ ، and the details of which appear a little later in the section. In the words لا إله إلا ھو (Allah: there is no god but He) which follow immediately, the [[doctrine]] of the Oneness of Allah has been put forth as a categorical declaration. It means that there is absolutely nothing worthy of worship other than Allah. | |||
Then come the words الْحَيُّ الْقَيُّومُ (the Alive, the All-Sustaining) which lay out a rational proof of the Oneness of Allah. The essence of the argument is that worship means to present oneself before somebody in [[utter]] submission and [[humility]]. It, therefore, requires that the one who is being worshipped must occupy the highest point of honour and power and who has to be most perfect from all angles. From this it is obvious that anything which cannot sustain its own being, rather is dependent upon somebody else for its very existence, could hardly claim to have any honour or power in its own right. Therefore, it is [[crystal clear]][https://en.wiktionary.org/wiki/crystal_clear] that all things in this world which have no power to come into being by themselves, nor can they sustain it - be they idols carved in stone, or water, or trees, or angels and apostles - none of them is worthy of worship. The only Being worthy of worship is the One who has always been Alive and Present and shall always live and sustain. Such a Being is none but Allah; there is none worthy of worship but Him. | |||
== You are reading a Tazkirul Quran tafsir for the group of verses 3:1 to 3:4 [https://quran.com/3:2/tafsirs/tazkirul-quran-en] == | |||
The Creator and Sustainer of the universe is not a [[mechanical]] God. He is, in fact, a live and conscious Being. | |||
He has sent guidance for man throughout the ages, including the Torah and the Bible, which were revealed to the former prophets. But man has always put different constructions upon divine teachings. Thus, through his self-styled interpretations, he has divided one religion into many. Ultimately, in accordance with God’s plan, the final book in the form of the Quran was sent down to man. The Quran is not only a genuine book of guidance but also serves as the criterion or standard of right and wrong. It tells us which is the true religion and which is the religion [[devised]] by human beings through [[misinterpretation]]. | |||
Now those who, denying the book of the Almighty, refuse to abandon the religion devised by human beings, are deserving of His punishment. These are the people to whom God granted eyes, but who failed to see the light (sent by God in the form of this book). These are the people to whom their Creator granted minds, but who failed to understand the truth when it came to them in the form of arguments. Bowing to the truth required them to bow to the Prophet and to God, and they thought that by [[surrendering]] to the Supreme Being and His Prophet they would [[diminish]] in stature. To save their petty ‘greatness’, they refused to bow to the Truth. | |||
== Tafsirin ayoyin 1-5 na Surar Ali Imran == | == Tafsirin ayoyin 1-5 na Surar Ali Imran == | ||
Allah ya bude wannan Sura da harrufa kamar yadda ya yi a Baqara, domin bayanin [[mu'ujizar]] Alƙur'ani, don nuna babu mai iya kawo kamarsa, duk kuwa da cewa magana ce da ta kunshi haruffa na Larabawa irin wadanda suke rubutu da su. Sannan Allah ya yi bayanin Allantakarsa da cewa, shi ne abin bauta na gaskiya, wanda daga cikin siffofinsa, shi ne Rayayye, mai cikakkiyar rayuwa, wadda ta siffantu da dukkan siffofi na kamala, Tsayayye da Zatinsa, ba shi da bukata a wurin wani cikin halittarsa, kuma shi ne mai tsayawa da taimakon kowa da komai, don haka kowa yana da bukata a wurinsa. Daga cikin taimakonsa da rahamarsa ga bayinsa, shi ne ya aiko musu da Annabi SAW, ya kuma saukar masa da Alkur'ani, wanda yake cike da gaskiya, kuma yake gaskata littattafan da suka gabace shi. Kuma Allah ya saukar da Attaura ga Annabi Musa (alaihissalam) da Linjila ga Annabi Isa (aS) tun kafin saukar da Alkur'ani. Allah ya saukar da littattafan nan ne dukkansu saboda shiriyar da mutane. A cikinsu Allah ya saukar da bin da yake bambancewa tsakanin ƙarya da gaskiya da tsakanin shiriya da ɓata, saboda haka Allah ya yi alkawarin azaba mai tsanani ga wadanda suka kafirce wa ayoyinsa a ranar gobe kiyama. Allah SWT babu wanda zai iya rinjayar sa, kuma babu abin da zai gagare shi, kuma shi mai gaggawar daukar fansa ne ga wanda ya saba masa. | Allah ya bude wannan Sura da harrufa kamar yadda ya yi a Baqara, domin bayanin [[mu'ujizar]] Alƙur'ani, don nuna babu mai iya kawo kamarsa, duk kuwa da cewa magana ce da ta kunshi haruffa na Larabawa irin wadanda suke rubutu da su. | ||
Sannan Allah ya yi bayanin Allantakarsa da cewa, shi ne abin bauta na gaskiya, wanda daga cikin siffofinsa, shi ne Rayayye, mai cikakkiyar rayuwa, wadda ta siffantu da dukkan siffofi na kamala, Tsayayye da Zatinsa, ba shi da bukata a wurin wani cikin halittarsa, kuma shi ne mai tsayawa da taimakon kowa da komai, don haka kowa yana da bukata a wurinsa. | |||
Daga cikin taimakonsa da rahamarsa ga bayinsa, shi ne ya aiko musu da Annabi SAW, ya kuma saukar masa da Alkur'ani, wanda yake cike da gaskiya, kuma yake gaskata littattafan da suka gabace shi. Kuma Allah ya saukar da Attaura ga Annabi Musa (alaihissalam) da Linjila ga Annabi Isa (aS) tun kafin saukar da Alkur'ani. Allah ya saukar da littattafan nan ne dukkansu saboda shiriyar da mutane. A cikinsu Allah ya saukar da bin da yake bambancewa tsakanin ƙarya da gaskiya da tsakanin shiriya da ɓata, saboda haka Allah ya yi alkawarin azaba mai tsanani ga wadanda suka kafirce wa ayoyinsa a ranar gobe kiyama. Allah SWT babu wanda zai iya rinjayar sa, kuma babu abin da zai gagare shi, kuma shi mai gaggawar daukar fansa ne ga wanda ya saba masa. | |||
Line 456: | Line 479: | ||
# Ga ku nan ku wadannan kun yi jayayya kan abin da kuke da ilimi a kai, to don me kuma kuke jayayya a kan abin da ba ku da ilimi a kansa? Kuma Allah Yana sane ku ba ku sani ba. --Quran/3/66 | # Ga ku nan ku wadannan kun yi jayayya kan abin da kuke da ilimi a kai, to don me kuma kuke jayayya a kan abin da ba ku da ilimi a kansa? Kuma Allah Yana sane ku ba ku sani ba. --Quran/3/66 | ||
# Ibrahim bai taɓa zama Bayahude ba, sannan bai taɓa zama Banasare ba, sai dai ya kasance mai barin ɓarna ne, Musulmi, kuma bai kasance ɗaya daga cikin mushrikai ba. --Quran/3/67 | # Ibrahim bai taɓa zama Bayahude ba, sannan bai taɓa zama Banasare ba, sai dai ya kasance mai barin ɓarna ne, Musulmi, kuma bai kasance ɗaya daga cikin mushrikai ba. --Quran/3/67 | ||
# Lalle mafi kusancin mutane da Ibrahim su ne wadanda suka bi shi, sai kuma wannan Annabin, da kuma wadanda suka yi Imani. Kuma Allah shi ne Majiɓincin al'amuran muminai. | # Lalle mafi kusancin mutane da Ibrahim su ne wadanda suka bi shi, sai kuma wannan Annabin, da kuma wadanda suka yi Imani. Kuma Allah shi ne Majiɓincin al'amuran muminai. --Quran/3/68 | ||
Bayan an kira Ma'abota Littafi zuwa ga addu'ar tsinuwa amma sun ƙi yarda, sannan an kawo musu hujjoji iri-iri wadanda suka nuna bacin addinin da suke kai, sun kuma kasa kare ɓatansu, kuma Allah ya riga ya san yadda Annabi yake maukar tausayin su, yana kwadayin shiriyarsu, sai Allah ya umarce shi da ya kirawo su gaba daya zuwa ga kalma ta bai-ɗaya, wadda kowa da kowa zai daidaita a kanta, kuma za su hada kai a kanta. Wannan kalma ita ce kadaita Allah da bauta, watau kada a bauta wa wani ba shi ba, mala'ika ne, ko wani annabi, ko waliyyi, ko wani gunki. Kada kuma su dauki wasu iayen giji, suna bauta musu ba Allah ba, har su riƙa halatta musu haram ko su haramta musu halal su kuma yarda. To idan sun bijire, sun ƙi yarda da wannan kiran; to ku muminai ku kafa su shaida cewa, ku Musulmi ne, kuma za ku ci gaba da bin wannan addinin da Allah ya zaɓa muku. | Bayan an kira Ma'abota Littafi zuwa ga addu'ar tsinuwa amma sun ƙi yarda, sannan an kawo musu hujjoji iri-iri wadanda suka nuna bacin addinin da suke kai, sun kuma kasa kare ɓatansu, kuma Allah ya riga ya san yadda Annabi yake maukar tausayin su, yana kwadayin shiriyarsu, sai Allah ya umarce shi da ya kirawo su gaba daya zuwa ga kalma ta bai-ɗaya, wadda kowa da kowa zai daidaita a kanta, kuma za su hada kai a kanta. Wannan kalma ita ce kadaita Allah da bauta, watau kada a bauta wa wani ba shi ba, mala'ika ne, ko wani annabi, ko waliyyi, ko wani gunki. Kada kuma su dauki wasu iayen giji, suna bauta musu ba Allah ba, har su riƙa halatta musu haram ko su haramta musu halal su kuma yarda. To idan sun bijire, sun ƙi yarda da wannan kiran; to ku muminai ku kafa su shaida cewa, ku Musulmi ne, kuma za ku ci gaba da bin wannan addinin da Allah ya zaɓa muku. | ||
Sannan Allah ya fuskantar da maganarsa ga Yahudawa da Nasara cewa, don mene ne suke jayayya game da lamarin Annabi Ibrahim; kowanne yana da'awar cewa a kan addininsa yake, Yahudawa suna cewa shi Bayahude ne, Nasara ma suna cewa shi Banasare ne, alhalin yadda gaskiyar al'amarin take, litafin Attaura da littafin Linjila, ba a saukar da su ba sai bayan mutuwarsa da lokaci mai tsawo. Yanzu ba za su yi aiki da hankulansu ba, su gane cewa, abin da suke fada karya ne? To ga shi yanzu su Yahudu da Nasara suna jayayya a kan abin da suke da ilimi a kansa na al'amarin addininsu, da abin da aka ambata a littafansu. To amma me ya sa | Sannan Allah ya fuskantar da maganarsa ga Yahudawa da Nasara cewa, don mene ne suke jayayya game da lamarin Annabi Ibrahim; kowanne yana da'awar cewa a kan addininsa yake, Yahudawa suna cewa shi Bayahude ne, Nasara ma suna cewa shi Banasare ne, alhalin yadda gaskiyar al'amarin take, litafin Attaura da littafin Linjila, ba a saukar da su ba sai bayan mutuwarsa da lokaci mai tsawo. Yanzu ba za su yi aiki da hankulansu ba, su gane cewa, abin da suke fada karya ne? To ga shi yanzu su Yahudu da Nasara suna jayayya a kan abin da suke da ilimi a kansa na al'amarin addininsu, da abin da aka ambata a littafansu. To amma me ya sa za su rika jayayya a kan abin da ba su da ilimi a kansa na lamarin Annabi Ibrahim, da addinin da ya rayu a kansa? Allah kam iliminsa ya kewaye komai, ya san abin da su ba su sani ba, amma su ba su san komai ba daga abin da Allah ya sani. | ||
Allah kuma ya bayyana musu gaskiyar al'amarin Annabi Ibrahim ya karyata maganar cewa shi Bayahude ne, ko Banasare. Allah ya tabbatar da cewa, Annabi Ibrahim tsaye yake ƙyam a kan addinin gaskiya, ba ruwansa da duk wata barna da shirka, yana bin umarnin Allah cikin ikhlasi, kuma ba ya cikin masu hada Allah da wani, masu bautar gumaka. | Allah kuma ya bayyana musu gaskiyar al'amarin Annabi Ibrahim ya karyata maganar cewa shi Bayahude ne, ko Banasare. Allah ya tabbatar da cewa, Annabi Ibrahim tsaye yake ƙyam a kan addinin gaskiya, ba ruwansa da duk wata barna da shirka, yana bin umarnin Allah cikin ikhlasi, kuma ba ya cikin masu hada Allah da wani, masu bautar gumaka. | ||
Sannan Allah ya ambaci wadanda suka fi cancantar su zama tare da Annabi Ibrahim, ya bayyana cewa, su ne wadanda suka bi addininsa, suka kuma bi hanyarsa ta kaɗaita Allah a wajen bauta, wadanda su ne Annabi, da sahabbansa, da muminai da za su zo bayansu. To wadannan su suka fi cancanta su zama masoyansa, majibintansa, kuma Allah shi ne yake jibintar lamarin muminai, ya taimaka musu, ya ba su nasara a kan abokan gabarsu. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Ya kamata Musulmi ya rika alfahari da cewa, shi Musulmi ne a ko'ina, kuma a gaban kowane ne. Ba kamar yadda wasu raunanan Musulmi suke jin kunyar su ce su Musulmai ne a gaban wadanda ba Musulmai ba. | |||
# Adalci yayin tattaunawa da wanda ba Musulmi ba dole ne, balle kuma tare da wanda yake Musulmi ne. | |||
# Amfanin karantar tarihi, domin zai taimaka wajen rushe ƙarairayi da dama waɗanda suka saɓa wa abin da ya tabbata a tarihi. | |||
# Kafa hujja da hankali a kan gaskiya, kuma duk wani lafiyayyen hankali idan mai shi ya yi amfani da shi; to zai kai shi ga fahimtar gaskiya. Sai dai ba daidai ba ne mutum ya dogara a kan hankalinsa gaba daya, ya watsar da nassi. | |||
# Imani shi ne musabbabin jibinta ta Ubangiji ga bawansa. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 69-71 == | |||
# Wata ƙungiya daga cikin Ma'abota Littafi sun yi burin ina ma sun ɓatar da ku, kuma ba za su batar da kowa ba sai kawunansu, amma ba sa fahimtar hakan. --Quran/3/69 | |||
# Ya ku Ma'abota Littafi, don me kuke kafice wa ayoyin Allah, alhalin kuna shaidawa (cewa gaskiya ne)? --Quran/3/70 | |||
# Ya ku Ma'abota Littafi, don me kuke cakuɗa gaskiya da ƙarya, kuma kuke boye gaskiya, alhalin kuna sane? --Quran/3/71 | |||
Allah a nan yana gargadin bayinsa muminai ne game da makircin wata kungiya ta Yahudawa da Nasara, wadanda ba su da wani buri a rayuwarsu, sai na ganin Musulmai sun lalace sun bace, sun yi watsi da addininsu na Musulunci, ba don komai ba sai don hassada da suke nuna musu. Sai dai makircinsu su kadai zai ci, domin kansu kawai suke kara batarwa, don haka duk kokarin da suke yi na batar da Musulmi yana komawa ne a kansu, suna kara dulmiya ne cikin bata da taɓewa, amma su ba su san hakan ba. | |||
Sannan Allah ya soki abin da Ma'abota Littafi ke aikatawa, yana cewa, don me suke kafirce wa Alkurani, alhalin sun san gaskiya ne, suna kuma shaidawa a kan hakan, domin sun karanta siffofin Annabi a littattafansu? Kuma don me suke cakuda karya da gaskiya, har a kasa bambancewa tsakaninsu, kuma su boye gaskiya alhalin suna sane da barnar da suke yi? | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Duk azzalumi akan saka masa da irin zaluncinsa, ko a jarrabe shi da irin cutar da yake kokarin ya yi wa wasu. | |||
# Mutum yakan makance ya kasa ganin ɓatan da yake ciki. | |||
# Wajibi ne a yi taka-tsantsan da mabarnata yayin da suka gauraya ƙarya da gaskiya, kuma kada a ruɗu da daɗin bakinsu. | |||
# Kakkausar suka ga duk mai cakuda karya da gaskiya, kuma yake boye gaskiya. Domin ambaton Ma'abota Littafi a nan, ba don ana nufin sai su kadai ba; duk wanda ya yi irin wannan aiki ya shiga cikin wannan sukar. | |||
# Taƙarƙarwar da Yahudu da Nasara suka yi wajen ganin sun batar da Musulmi shi ya hana su su bi gaskiya, domin duk sa'adda mutum ya dage kan wani mugun abu; to sai ya manta da abin da wannan abin kan iya haifar masa nan gaba. | |||
# Mai boye gaskiya ba shi da wata hanyar yin hakan sai ta fuskoki biyu: | |||
## Fuska ta Farko: Ya jeho wani abu mai rikitarwa don ya tabbatar da karya. | |||
## Fuska ta Biyu: Ya boye duk wani dalili da zai fito da gaskiya. | |||
# Haɗa ƙarya da gaskiya shi ne sanadiyyar ɓacewar al'ummomin da suka gabace mu, kuma shi ne mafarar duk wata [[bidi'a]], domin ita bidi'a, da a ce karya ce [[tsantsarta]]; to ba za ta samu karbuwa ba, da kowa ya yi watsi da ita; da kuma a ce gaskiya ce tsantsa, to da ba ta zama bidi'a ba, da ta zama daidai da Sunna. Sai dai an gauraya karya ce da gaskiya wuri guda, sai wasu su kasa gane karyar da ke cikinta. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 72-74 == | |||
# Kuma wata ƙungiya cikin Ma'abota Littafi suka ce: "Ku yi imani mana da abin da aka saukar wa wadanda suka yi imani a farkon yini, kuma ku kafirce a karshen yini, mai yiwuwa ne su dawo (daga rakiyar addininsu). --Quran/3/72 | |||
# "Kuma kada ku amince da kowa sai wanda ya bi addininku." Ka ce: "Lalle shiriya ita ce Allah, domin kar (ku yarda a ce) an ba wani mutum irin abin da aka ba ku, ko kuma ku ba su dama su yi jayayya da ku a wajen Ubangijinku." Ka ce: "Lalle falala a hannun Allah take, Yana bayar da ita ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mai yalwa ne, Mai yawan sani. --Quran/3/73 | |||
# "Yana keɓantar wanda Ya ga dama da rahamarsa, kuma Allah Ma'abocin falala ne wadda take mai girma." --Quran/3/74 | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana ba da labarin wasu miyagun mutane ne a cikin Yahudawa da Nasara, wadanda suke ta ƙulle-ƙullen makirci ga Musulmi ta hanyar kawo ruɗu na addini ga wasu raunanan Musulmi. Sun yanke shawara a tsakaninsu cewa, su bayyana imaninsu da abin da Manzon Allah ya zo da shi a farkon yini; idan yamma ta yi kuma su kafirce masa. Yin haka shi zai sa masu raunin [[fahinta]] cikin muminai su rika cewa, da a ce gaskiya ne, da wadanda suka yi imani da shi cikin Ma'abota Littafi, ba su yi ridda ba. Manufarsu ita ce Musulmi su watsar da addininsu gaba daya. | |||
Sannan magana ta dawo kan tattaunawar Yahudawa a tsakaninsu, da irin yadda suke yi wa junansu wasiyya, yayin da wasunsu sika faɗa wa wasu cewa, kada su yarda da kowa idan ba wanda yake bin addininsu ba, kada kuma su yarda su bayyana sirrinsu ga wani Musulmi don kada ya samu irin ilimin abin da suka samu; idan har sun yi haka to za su koye shi, su ma sai su zama masu ilimi ko kuma su riƙe shi a matsayin abin da za su kafa musu hujja da shi a gaban Allah, sai su ba da shaidar cewa, gaskiya ta bayyana gare su, ƙin bi suka yi. Sai Allah ya ce wa Annabinsa ya faɗa musu cewa, shiriya a hannun Allah take, yana bayar da ita ga wanda ya ga dama daga bayinsa. Kuma Allah mai yalwar falala ne, mai yawan kyauta, kuma mai cikakken sani ne game da wadanda suka cancanci a kyautata musu, don haka yana yin kyautarsa ne ga wanda ya cancanta, ya kuma hana wanda bai cancanta ba kuma yana keɓance wanda ya ga dama da rahamarsa, kuma shi ma'abocin falala ne mai yawa. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Gargadin Musulmin da ake amfani da su don jefa shakka a cikin zukatan raunanansu, ta hanyar yi wa Musulunci tuhumce-tuhumce iri-iri don a ɓata shi a idon 'ya'yansa, a ɓata tarihinsa da koyarwarsa da nassoshinsa. Ta hanyar sunaye wadannan raunanan mutane suke nuna su Musulmi ne, amma suna taka rawa a gefe guda irin ta Yahudawa. | |||
# Wanda duk ya nemi shiriya ba ta hanyar Alƙur'ani da sunna ba; to ya ɓace, domin babu shiriya sai wadda Manzon Allah ya zo da ita. | |||
# Amfanin ba da labarin wannan makirci na Yahudawa na cewa su yi imani da farkon yini, daga ƙarshensa sai su yi ridda. Amfanin fallasa su shi ne: | |||
## Na daya: wannan shirin nasu sun yi ne a boye, ba wani Musulmi da ya san da shi; to yayin da Manzon Allah ya zo yana ba da labarin wannan sirri nasu, hakan ya nuna cewa lalle shi Manzon Allah ne, domin ya ba da labarin wani abu da ba wanda ya san shi sai Allah da ya sanar da shi. | |||
## Na biyu: Bayan Allah ya fallasa wannan mugun shiri nasu; sai ya zama ba zai yi wani tasiri ba a zukatan muminai, don ba don haka ba, da watakila a ga tasirinsa a wurin wasu masu raunin imani. | |||
## Na uku: Za su ji tsoron kara kulla wani makircin irin wannan bayan Allah ya tona asirinsu. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 75-76 == | |||
# Kuma daga cikin Ma'abota Littafi akwai wanda in da za ka ba shi amana ta dukiya mai yawa, zai dawo maka da ita, daga cikinsu kuwa akwai wanda idan an ba shi amana ta dinare ɗaya, ba zai dawo maka da shi ba, sai fa idan ka tashi tsaye a kansa. Wannan kuwa saboda sun ce: "Babu wani laifi a kanmu (don mun ci dukiyar) bobayin mutane." Kuma suna fadin karya su jingina wa Allah, alhalin su suna sane. | |||
# Ba haka ba ne, duk wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya tsare dokar Allah, to lalle Allah Yana son masu taqawa. | |||
Bayan Allah ya bayyana mana irin karyar da Yahudawa suke yi na cewa an ba su matsayi na ilimi da addini wanda ba wanda aka ba irinsa, da kuma nuna cewa bin addininsu kadai shi ne shiriya, sai Allah a nan ya karyata su, ya nuna su a matsayin maciya amana, wadanda mu'amalarsu da mutane babu gaskiya a cikinta, kamar yadda mu'amalarsu da Allah ita ma babu gaskiya a cikinta ko kadan. | |||
Allah ya bayyana cewa, a cikin ma'abota Littafi akwai mai amana, wanda idan da za ka ba shi amanar dukiya komai yawanta, ba zai ci komai daga cikinta ba, zai dawo maka da ita kamar yadda ka ba shi. Daga cikinsu kuma akwai maci amana wanda da za ka ba shi dan kudi kadan, kamar Dinari daya; to ba zai taɓa dawo maka da kayanka ba, sai ka yi tsayuwar daka a kansa, ka matsa masa, sannan zai dawo da shi. | |||
Sai kuma Allah ya bayyana dalilin wannan mugun hali nasu da cewa, saboda suna riyawa ne cewa, ba su da wani laifi don sun ci dukiyar wadanda ba Yahudawa ba, wato suna nufin Musulmi. Watau a nan sun hada laifuka biyu: Laifin cin dukiyar haram da kuma laifin halatta haram. To wannan ita ce karyar da suka yi wa Allah, alhalin sun san karya suke. | |||
Sannan Allah ya rushe wannan da'awar tasu, da cewa, al'amarin ba haka yake ba. Duk wani Bayahude ko Banasare idan ya cika alkawarin da Allah ya yi da su, ya yi imani da Annabi SAW da Alkur'anin da ya saukar masa, ya kiyaye dokokin Allah ta hanyar aikata abin da aka umarce shi da barin abin da aka hana shi; to lalle ya sani Allah yana son masu taqawa cikin bayinsa. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# A cikin Ma'abota Littafi da mushrikai za a iya samun masu amana, don haka ana iya ba wa ɗayansu amanar dukiya. Ya halatta Musulmi ya dauki kafiri mai amana aikin likitanci, domin wannan yana daga cikin karbar labarin abin da suka sani na sha'anin duniya. Wannan ya halatta, sai dai idan an hango wata barna; to sai a kauce mata. Duk da halaccin yin haka amma mu'amala da Musulmi mai amana ta fi. | |||
# Wanda duk ya yi wa Allah karya yana sane, ya fi girman zunubi, fiye da wanda ya yi masa karya bisa ga rashin sani. | |||
# Wanda duk ya cika alkawarin da ya daukar wa Allah, ya guji karya ko yaudara; to Allah zai so shi, ya yi masa rahama duniya da lahira. | |||
# Cika alkawarin Allah ya kunshi alkawarin da ke tsakaninsa da bawansa na bauta masa, da ba shi hakkokinsa, da kuma alkawarin da ke tsakanin bawa da sauran 'yan'uwansa bayi. | |||
# Tsoron Allah da bawa zai siffanta da shi, shi ne zai sa Allah ya so shi. | |||
# Duk wata mu'amala mai kyau da bawa zai yi; to ya yi domin neman yardar Allah, da haka ne Allah zai saka masa da soyayyarsa gare shi. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 77-80 == | |||
# Lalle wadanda suke [[musanya]] alkawarin Allah da rantse-rantsensu da wani dan farashi [[ƙanƙani]], wadannan ba su da wani rabo a lahira, kuma Allah ba zai yi musu magana ba, kuma ba zai dube su (duba na rahama) ba a ranar alkiyama, kuma ba zai tsarkake su ba, kuma suna da azaba mai radadi. --Quran/3/77 | |||
#Kuma lalle daga cikinsu akwai wani bangare da suke karkatar da harshensu lokacin karanta Littafin (Attaura), don ku yi zaton yana cikin Littafin, alhali kuwa ba ya cikin Littafin, kuma za su rika cewa, shi (wahayi ne saukakke) daga wurin Allah, alhalin kuwa ba daga wurin Allah yake ba, kuma za su rika [[faɗar]] ƙarya suna jingina wa Allah, alhalin suna sane. --Quran/3/78 | |||
#Bai dace ba ga wani mutum wanda Allah zai ba shi littafi da hukunci da annabci, sannan ya ce wa mutane: "Ku zama bayina ba na Allah ba," sai dai (ya ce): "Ku zamo malamai na Allah saboda abin da kuke karantarwa na littafi, kuma saboda abin da kuka kasance kuna karantawa." --Quran/3/79 | |||
#Kuma ba zai umarce ku da ku riki mala'iku ko annabawa a matsayin iyayengiji ba; yanzu zai umarce ku da kafirci ne bayan kuna Musulmi? --Quran/3/80 | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana ba da labarin irin uƙubar da ya tanadar wa wadanda suke karya alkawarin da suka yi tsakaninsu da shi, su canja shi don wani abu na duniya da bai taka kara ya karya ba, maimakon su yi biyayya ga Annabi, su yi imani da shi, sai su rika rantsuwar karya don su samu wani abin duniya. Allah ya ce, wadannan ne ba su da wani rabo na alheri a lahira, kuma Allah ba zai yi magana da su ba, kuma ba zai dube su ba, sannan ba zai tsarkake su daga zunubansu ba, kuma suna da wata azaba mai radadi. | |||
Abdullahi dan Mas'ud ya ce: Wanda ya yi rantsuwa don ya ci wata dukiya da ba tasa ba; to zai haɗu da Allah yana mai fushi da shi. Sai Allah ya gaskata wannan magana tasa, ya saukar da wannan ayar: "Lalle wadanda suke [[musanya]] alkawarin Allah da rantse-rantsensu da wani dan farashi [[ƙanƙani]],..." har zuwa karshen ayar. | |||
Abdullah (bin Mas'ud) said, "Whoever took a false oath in order to grab somebody's property will meet Allah while Allah will be angry with him." Allah revealed the following verse to confirm that:--"Verily! Those who purchase a small gain at the cost of Allah's covenant And their oaths...a painful torment." (3.77) | |||
Abu Wa'il ya ce: Sai Al-Ash'as dan Qais ya fito gare mu ya ce: Me Abu Abdurrahman yake fada muku (yana nufin Ibn Mas'ud)? | |||
Al-Ash'ath bin Qais came to us and asked as to what Abu Abdur-Rehman (i.e. Ibn Mas'ud) was telling you." | |||
Sai muka fada masa. Sai ya ce: "Gaskiya ya fada, a kaina wannan ayar ta sauka. Mun yi rigima da wani mutum a kan wata rijiya, sai muka je gaban Annabi SAW domin ya yi mana hukunci, | |||
We related the story to him. On that he said, "He has told the truth. This verse was revealed about me. I had some dispute with another man regarding a well and we took the case before Allah's Messenger (ﷺ). | |||
sai Manzon Allah ya ce: "Kawo shaidunka biyu, ko kuma shi ya rantse." | |||
Allah's Messenger (ﷺ) said (to me), "Produce two witnesses (to support your claim); otherwise the defendant has the right to take an oath (to refute your claim).' | |||
Sai na ce: In dai haka ne; to fa shi zai rantse ba tare da ya damu ba. | |||
I said, 'The defendant would not mind to take a false oath." | |||
Sai Manzon Allah ya ce: "Duk wanda ya yi rantsuwa don ya cancanci wata dukiya alhalin ƙarya yake; to zai haɗu da Allah alhalin yana mai fushi da shi." | |||
Allah's Messenger (ﷺ) then said, 'Whoever took a false oath in order to grab someone else's property will meet Allah, Allah will be angry with him.' | |||
Sai Allah ya gaskata wannan magana, ya saukar da wannan ayar. [Bukhari #2515-2516 da Muslim #136]. | |||
Allah then revealed what Confirmed it." Al-Ash'ath then recited the following Verse:--"Verily! Those who purchase a small gain at the cost of Allah's covenant, And their oaths . . . (to) . . . they shall have a painful torment!' (3.77) (See Hadith No. 546) https://sunnah.com/bukhari:2515 | |||
Abdullahi dan Abu Aufa yana cewa: Wani mutum a kasuwa, ya tsaya a kan hajarsa yana rantsuwar cewa, an saya da kudi kaza da kaza, alhalin karya yake, don kawaiya zurma wani Musulmi. Sai Allah ya saukar da wannan ayar. [Bukhari #2088]. | |||
Babu cin karo tsakanin ruwayoyin nan guda 2, domin zai iya yiwuwa ayar ta sauka a kan kissoshin biyu. | |||
Sannan Allah ya bayyana wa muminai halin wasu mutane daga cikin Yahudu da Nasara cewa, idan suna karanta littafin da aka saukar musu, sai su rika karkata harshensu suna jirkita wasu lafuzan littafin, suna wasa da ma'anoninsa, da nufin ɓatar da muminai, don su zaci cewa maganar Allah ce abin da suke karantawa, alhalin ba ita ba ce; kawai wannan wata bidi'a ce suka shigo da ita a cikin addini. Da wannan aiki nasu, suna yi wa Allah karya ne tare da suna sani. | |||
Sai kuma Allah ya bayyana cewa, ba abu ne mai yiwuwa ba, Allah ya zaɓi wani mutum, ya ba shi littafi da hikima, ya yi masa baiwar annabci, sannan ya rika kiran mutane kan su bauta masa ba Allah ba. Idan har Allah ya yi wa wasu bayinsa irin wannan baiwa; to zai umarce su ne da su zamo malamai na Allah, masu aiki da iliminsu, masu ikhlasie da bautar Allah, suna koyar da mutane ilimi da tarbiyya ta kwarai, saboda littafin Allah ne suke koyarwa. Hakanan kuma ba zai umarce su su rika bauta wa mala'iku ko annabawa, ba Allah ba. Domin babu yadda za a yi ya umarce su da su kafirce wa Allah bayan sun musulunta, sun mika wuya ga Allah. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Wanda ya tilasta wa mutane su bi maganarsa, su yi masa ɗa'a a kowanne hali; to ya zama mai kiran su ne su bauta masa, ba Allah ba. | |||
# Ya kamata mutum ya zama mai koyar da ilimi, kuma malami na Allah, domin duk malamin da ba na Allah ba; to iliminsa na banza ne ba zai amfane shi da komai ba. | |||
# Bayanin kafircin wadanda yake bauta wa mala'iku ko annabawa ko waliyyai ko kuma malamai. | |||
# Karya alkawari da yarjejeniya yana daga cikin manya-manyan abubuwan da suke kawo matsala a zamantakewar al'umma, shi ya sa Allah ya yi alkawarin narko mai tsanani ga wadanda suke karya alkawali. | |||
# Malami ba shi ne wanda ya cika ƙwaƙwalen mutane da ilimi ba kawai, a'a dole sai ya hada da yi musu tarbiyya ta kwarai. | |||
# Allah ya tsoratar da masu sayen wani abin duniya da alkawarin da ke tsakaninsu da Allah. Malamai masu boye gaskiya don wani abin duniya sun shiga cikin wannan gargadi. | |||
# Hukuncin alkali ba ya halatta haram. Don haka ko alkali ya yi hukuncin danka dukiyar wani ga wanda ba tasa ba, saboda abin da ya bayyana gare shi na dalilai, to wannan ba ya halatta masa wannan abin. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 81-82 == | |||
#Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya yi alkawari da annabawa cewa: "Duk irin abin da Na ba ku na littafi da wata hikima, sannan sai wani Manzo ya zo muku mai gaskata abin da yake tare da ku, to lalle ku yi imani da shi, kuma lalle ku taimake shi." Ya ce: "Shin kun yarda da hakan, kuma kun dauki alkawarina a kan hakan?" Suka ce: "Mun yarda da haka." Ya ce: "To ku shaida, kuma Ni ma Ina tare da ku cikin masu shaidawa." --Quran/3/81 | |||
#To duk wanda ya juya baya bayan wannan, to wadannan sune fasikai. --Quran/3/82 | |||
A wadannan ayoyi Allah yana tunatar da Annabinsa lokacin da ya dauki alkawari mai karfi tsakaninsa da annabawa cewa, duk da annabcin da ya aiko su da shi da littattafai da hikima da ya ba su, sannan daga baya ya aiko da wani manzo ya zo musu, su da al'ummominsu, yana tabbatar da gaskiyar da suka zo da ita, to wajibi ne su yi imani da shi su gaskata abin da ya zo da shi, su taimaka masa. Ana nufin Manzon Allah Muhammadu SAW. Sannan Allah SWT ya ƙara ƙarfafa musu cewa, sun yarda da wannan alƙawari, kuma sun riƙe shi da ƙarfi?! Dukkansu suka amsa da cewa, sun yarda kuma sun tabbata. Sai Allah ya kafa su da su zama masu shaidar kansu da kansu akan haka da kuma al'ummominsu. Duk kuma wanda ya bijire bayan wannan alƙawari da ya ɗauka; to masu yin haka su ne fasikai, wadanda suka fita daga ɗa'ar Allah. | |||
Jabir ɗan Abdullahi ya ruwaito cewa, Manzon Allah ya ce: "Da a ce ɗan'uwana Musa yana nan da ransa, da babu abin da zai [[fisshe]] shi, dole sai yi min biyayya." [Ahmad #5195]. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Falalar Annabi Muhammadu SAW a kan sauran annabawa. | |||
# Annabawa gaba dayansu bayi ne na Allah, masu bauta masa da bin umarninsa. | |||
# Idan ya zamana wajibi ne a kan annabawa su yi imani da Annabi SAW; to imanin al'ummominsu da shi ya fi zama wajibi a kansu. | |||
# Babu wata hanyar samun yardar Allah, sai ta hanyar bin Manzon Allah, ko da kuwa annabawa ne, da a ce suna da rai lokacin aiko Annabi Muhammad SAW; to sai sun yi imani da shi. | |||
# Wannan aya tana matsayin martani ga masu cewa Khadir yana nan da ransa bai mutu ba. Domin da wannan magana gaskiya ce, da ya zama wajibi a kansa ya bayyana a zamanin Annabi SAW, ya yi imani da shi, ya yi jihadi tare da shi, ya taimaka masa. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 83-85 == | |||
# To shin yanzu wani addini suke nema ba na Allah ba, alhalin duk wanda yake cikin sammai da ƙasa gare Shi ne ya mika wuya yana so ko yana ƙi, kuma zuwa gare Shi za a komar da su? --Quran/3/83 | |||
# Ka ce: "Mun yi imani da Allah da abin da aka saukar mana da kuma abin da aka saukar wa Ibrahimu da Isma'ila da Ishaq da Yaqoob da jikokin Yaqoob, da abin da aka ba wa Musa da Isa da abin da aka ba wa annabawa dafa Ubangijinsu; ba ma nuna bambanci a kan daya daga cikinsu, kuma mu muna masu mika wuya gare Shi." | |||
# Duk kuma wanda ya nemi (bin) wani addini ba Musulunci ba, to har abada ba za karba daga gare shi ba, kuma shi a lahira yana cikin hasararru. | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana bayyana cewa, duk wanda ya nemi wani addini ba Musuluncin da Allah ya aiko Annabinsa Muhammad sa shi ba; to ya yi aikin banza. Allah yana sukar duk wanda ya nemi wani addini ba na Allah ba, kuma ba shari'arsa ba, alhalin duk wadanda suke sama da wadanda suke ƙasa, gare shi suka mika wuya, sun so hakan, ko ba su so ba, duk suna karkashin ikonsa ne, shi ne mai sarrafa su yadda ya ga dama. Kuma idan suka mutu zuwa gare shi ne makomarsu take, zai yi wa kowa hisabi da gwargwadon aikinsa. | |||
Allah kuma ya fuskantar da maganarsa zuwa ga Annabi, yana umartar sa da ya gaya wa wadanda suke neman wani addini daban ba Musulunci ba cewa, mu mun yi imani da Allah da Alkur'anin da aka saukar mana, da kuma sunnah, da duk abin da Allah ya saukar wa annabawansa - Annabi Ibrahim da 'ya'yansa, Annabi Isma'ila da Annabi Ishaq da Yaqoob dan Ishaq, da kuma abin da aka saukar wa annabawan Banu Isra'ila, wadanda suka fito daga zurrriyar 'ya'yan Annabi Yaqoob, su goma sha biyu (12). Hakanan mun yi imani da littafin Attaura da Allah ya saukar wa Annabi Isa da kuma mu'ujizojin da Allah ya ba su domin tabbatar da gaskiyarsu. Mun yi imani da duk annabawa gaba dayansu, da abin da aka saukar musu na littattafai daga Ubangijinsu, ba za mu bambanta tsakaninsu ba wajen imani, ta hanyar yin imani, ta hanyar yin imani da wasu, mu kafirce wa wasu; mu gaba dayanmu ciki da waje, mun mika wuya ga Allah, ba za mu yarda da wani addini in ba Musulunci ba. | |||
Sannan Allah ya bayyana cewa, duk wanda ya bi wani addini ba na Musulunci ba; to ba za a taɓa karbar sa daga gare shi ba, kuma a lahira yana cikin hasararru, wannan kuma ita ce hasara ta hakika, domin ya wahalar da kansa a kan abin da bai amfane shi ba. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Musulunci shi kadai ne addini a wurin Allah. Wanda ya bi wani addini ba Musulunci ba; to Allah ba zai kaɓe shi daga wurinsa ba. | |||
# Dole ne a kan duk wani mai furuci, ya furta imaninsa da Allah da bakinsa, kamar yadda yake wajibi a kansa ya ƙudurce a zuciyarsa. | |||
# Imani da Allah shi ne asali, duk sauran abubuwa da bawa yake imani da su rassa ne nasa, shi ya sa Allah ya gabatar da shi a nan. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 86-89 == | |||
# Ta yaya Allah zai shiryar da mutanen da suka kafirta bayan imaninsu, kuma bayan sun shaida cewa, Manzon gaskiya ne, kuma hujjoji sun zo musu? Allah kuwa ba Ya shiryar da mutane azzalumai. | |||
# Wadannan sakamakonsu shi ne, la'antar Allah za ta tabbata a kansu da ta mala'iku da mutane gaba daya. | |||
# Suna masu dawwama a cikinta, ba za a sassauta musu azaba ba, kuma ba za jinkirta musu ba. | |||
# Sai fa wadanda suka sake tuba bayan haka, kuma suka gyara (ayyukansu), to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai. | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana bayyana cewa, ba zai shiryar da mutanen da suka yi ridda ba, suka juya wa MUsulunci baya, alhalin da farko sun yi imani, kuma sun tabbatar da cewa, Annabi Muhammad gaskiya ne, saboda hujjoji bayyanannu, kuma gamsassu, masu ƙara tabbatar da gaskiyarsa. Ta yaya irin wadannan za su cancanci shiriya? Allah ba ya shiryar da wadanda suka zalunci kawunansu, ta hanyar barin gaskiya bayan sun fahimce ta, suka kama ƙarya bayan sun gane ƙarya ce a fili. | |||
Sannan Allah ya faɗi uƙubar waɗannan azzaluman a duniya da lahira, wadda ita ce la'anar Allah da mala'iku da duk halittun Allah a kansu, kuma za su ci gaba da zama cikin wannan la'anar, da wannan ukubar, har abada, kuma ba za a taɓa sassauta musu azaba ba, kuma ba za a saurara musu ba. | |||
Amma sai Allah ya yi togaciya ta wadanda suka tuba, suka yi ayyuka na kwarai, kuma suka gyara kurakuren da suka yi; to wadannan Allah yana yafe musu, saboda shi mai yawan gafara ne, mai yawan jin kai ga bayinsa masu tuba su gyara. Abdullahi dan Abbas yana cewa: | |||
#''"Wani mutumin Madina ya musulunta,''<br>"A man from among the Ansar accepted Islam,<br><br> | |||
#''daga baya kuma sai ya yi [[ridda]], ya koma shirka.''<br>then he [[apostatized]] and went back to Shirk. <br><br> | |||
#''Sannan ya dawo ya yi [[nadama]], sai ya aika wa mutanensa yana cewa:''<br>Then he [[regretted]] that, and sent word to his people (saying): <br><br> | |||
#'' 'Ku tambayar mini Manzon Allah, shin zan iya sake [[tuba]]?' ''<br> 'Ask the Messenger of Allah [SAW], is there any [[repentance]] for me?' <br><br> | |||
#''Mutanensa suka sami Manzon Allah, suka faɗa masa cewa:''<br>His people came to the Messenger of Allah [SAW] and said: <br><br> | |||
#'' 'Wane da ya yi ridda ya yi nadama, kuma ya aiko mu mu tambaya masa cewa, shin zai iya sake tuba?' ''<br>'So and so regrets (what he did), and he has told us to ask you if there is any repentance for him?' <br><br> | |||
Sai wannan ayar ta sauka: 'Ta yaya Allah zai shiryar da mutanen da suka kafirta bayan imaninsu...' har inda ya ce: '...to lalle Allah mai gafara ne, mai jin kai.' Sai Annabi ya aika masa ya zo ya sake shiga Musulunci." [Nisa'i #4068 da Ahmad #2218]. | |||
Then the Verses: 'How shall Allah guide a people who disbelieved after their Belief up to His saying: Verily, Allah is Oft-Forgiving, Most Merciful' was revealed. So he sent word to him, and he accepted Islam." https://sunnah.com/nasai:4068 | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Ɓacewar mai ilimi ta fi ɓacewar jahili muni. | |||
# Jahili ya fi saurin mika wuya yayin da za a fahimtar da shi abin da bai fahinta ba, amma wanda ya sani ya kangare; to wannan yana da wuya ya dawo kan hanya. | |||
# Tubar bawa ba ta cika, har sai ya gyara barnar da ya yi a baya, ko da ta hanyar bayyana cewa abin da yake kai a baya ɓata ne, don ire-irensa su dawo, su ma su taba. Ko kuma idan ya ja wasu zuwa ga wannan ɓatan; to dole ne ya bayyana musu abin da suke a kai ɓata ne. | |||
# Duk wanda Allah ya yi wa wata ni'ima, sannan ya kafirce masa; to Allah na iya karbe wannan ni'imar daga hannunsa. | |||
# Wanda ya yi ridda, sannan daga baya ya tuba, ya gyaru; to Allah zai karbi tubansa a duniya da lahira. | |||
# Tuba yana kankare laifin da mai tuba ya yi a baya, ko da kuwa kafirci ne. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 90-91 == | |||
# Lalle wadanda suka kafirta bayan imaninsu, sannan suka ƙara zurfi cikin kafirci, to ba za a karbi tubansu ba, kuma wadannan su ne batattu. --Quran/3/90 | |||
# Lalle wadanda suka kafirta, kuma suka mutu alhali suna kafirai, to ba za a karbi cikin ƙasa na zinari daga daya daga cikinsu ba, ko da zai fanshi kansa da shi. Wadannan suna da wata azaba mai radadi kuma su da wasu mataimaka. | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana bayanin ukubar wadanda suka yi imani, sannan daga baya suka yi ridda, suka kafirta, sannan suka yi ƙara nutsawa cikin kafirci, suka kuma zauna a haka, har suka mutu cewa, Allah ba zai taɓa karɓar tubansu ba, domin su ne suka zaɓi su bar hanyar gaskiya, su bi hanyar ɓata. | |||
Sannan Allah ya kara tabbatar da cewa, wadanda suka kafirta, kuma suka mutu a kan kafirci, ba su tuba ba; to Allah ba zai karbi aikin da suka yi ba, ko da kuwa zai yi sadaka da kwatankwacin cikin ƙasa na zinariya domin ya kusanci Allah da wannan sadakar, Allah ba zai karba ba, ko kuma ya ce zai fanshi kansa da wannan, to Allah ba zai karba ba. Sakamakon wadannan a lahira shi ne azabar wuta mai radadi, kuma babu wanda ya isa ya kubutar da su daga wannan azabar. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Yadda imani yake ƙaruwa da ayyuka na ƙwarai, haka shi ma kafirci yake hauhawa da ƙaruwar aikata ayyukan kafirci. | |||
# Tubar mutum ba za ta zama karbabbiya ba a wurin Allah har sai ya bar laifukan da yake aikatawa, ya kuma gyara abin da ya bata a baya. | |||
#Mummunan aiki yana haddasa wani mummuna irinsa, matukar bawa bai dawo kan tafarki madaidaici ba. | |||
#Wanda ya yi ridda ya bar Musulunci har mutuwa ta zo masa bai tuba ba; to ba za a karbi tubansa ba a wannan lokacin. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 92 == | |||
# Ba za ku taɓa dacewa da aiki na alheri ba har sai kun ciyar daga abin da kuke so, kuma abin da duk kuka ciyar kowane iri ne, to lalle Allah Yana sane da shi. | |||
3:92 | |||
لَن تَنَالُوا۟ ٱلْبِرَّ حَتَّىٰ تُنفِقُوا۟ مِمَّا تُحِبُّونَ ۚ وَمَا تُنفِقُوا۟ مِن شَىْءٍۢ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٌۭ ٩٢ | |||
You will never achieve righteousness until you donate some of what you cherish. And whatever you give is certainly well known to Allah. | |||
— Dr. Mustafa Khattab, The Clear Quran | |||
Never will you attain the good [reward][1] until you spend [in the way of Allāh] from that which you love. And whatever you spend - indeed, Allāh is Knowing of it. | |||
— Saheeh International | |||
[1] Another meaning is "You will never attain righteousness." | |||
Lan tanaloo albirra hattatunfiqoo mimma tuhibboona wama tunfiqoo minshay-in fa-inna Allaha bihi AAaleem | |||
— Transliteration | |||
Bã zã ku sãmi kyautatãwa ba, sai kun ciyar daga abin da kuke so. Kuma abin da kuka ciyar, kõ mẽne ne, to, lalle ne Allah, gare shi, Masani ne. | |||
— Hausa Translation(Abubakar Gumi) | |||
Bayan Allah a ayar baya ya yi bayanin cewa, ba zai karbi sadakar kafiri ba, ko da zai ciyar da kwatankwacin cikin duniya na zinari, don ya kuɓutar da kansa daga azabar Allah a ranar alƙiyama, sai a wannan ayar Allah yake kwaɗaitar da muminai kan su ciyar da dukiyarsu, kuma ya bayyana cewa, abin da ya fi son bawa ya yi sadaka da shi, shi ne abin da shi ya fi so; wannan ne zai kai shi matakin samun alheri mai yawa. Allah yana cewa: "Ba za ku kai ga samun alheri mai yawa ba daga Allah, har sai kun yi sadaka da dukiyar da kuke ƙauna a zukatanku. Duk abin da kuka ciyar na dukiyarku; to Allah ya sani, kuma a ranar lahira zai saka wa wanda ya yi haka da cikakken sakamako." | |||
An karbo daga Anas dan Malik ya ce: | |||
# "Abu Talha mutumin Madina ne mai yawan dukiya; abin da kuma ya fi kauna cikin dukiyarsa ita ce gonarsa mai suna Bairuha, tana kallon masallacin Annabi.''<br>Abu Talha had the greatest wealth of date-palms amongst the Ansar in Medina, and he prized above all his wealth (his garden) Bairuha', which was situated opposite the Mosque (of the Prophet (ﷺ) ). <br><br> | |||
# Hasali ma Annabi yakan shiga cikinta ya sha ruwanta mai dadi.''<br>The Prophet used to enter It and drink from its fresh water. <br><br> | |||
# To lokacin da wannan ayar ta sauka... sai Abu Talha ya ce:''<br>When the following Divine Verse came:--(3.92) Abu Talha got up saying. <br><br> | |||
# "Ya Manzon Allah, Allah yana cewa: 'Ba za ku taba dacewa da aiki na alheri ba, har sai kun ciyar daga abin da kuke so...', "''<br>"O Allah's Messenger (ﷺ)! Allah says, 'You will not attain piety until you spend of what you love,' <br><br> | |||
# ni kuma a cikin dukiyata na fi son Bairuha, don haka na bayar da ita sadaka don Allah,''<br>and I prize above al I my wealth, Bairuha' which I want to give in charity for Allah's Sake, <br><br> | |||
# ina fatan alherinta da ajiyayyen ladanta a wurin Allah Ta'ala''<br>hoping for its reward from Allah. <br><br> | |||
# don haka ya Ma'aikin Allah, ka saka ta inda Allah Ta'ala ya nuna maka.''<br>So you can use it as Allah directs you."<br><br> | |||
# Sai Annabi ya ce: "Taɓdi! Wannan fa dukiya ce mai riba.''<br>On that the Prophet (ﷺ) said, "Bravo! It is a profitable (or perishable) property. (Ibn Maslama is not sure as to which word is right, i.e. profitable or perishable.) <br><br> | |||
# to lalle na ji abin da ka ce, amma ni ina ganin ka yi kyautarta ga danginka mafi kusanci da kai shi ya fi riba."''<br>I have heard what you have said, and I recommend that you distribute this amongst your relatives." <br><br> | |||
# Sai Abu Talha ya ce: "Ya Ma'aikin Allah! Zan yi hakan,''<br>On that Abu Talha said, "O Allah's Messenger (ﷺ)! I will do (as you have suggested)." <br><br> | |||
# Sai Abu Talha ya raba wa danginsa da 'ya'yan baffanninsa wannan gonar. [Bukhari #2769, Muslim #998, Ahmad #12461]''<br>So, Abu Talha distributed that garden amongst his relatives and cousins. https://sunnah.com/bukhari:2769 | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Kwaɗaitar da muminai a kan su nemi alheri, ta hanyar gabatar da soyayyarsu ga Allah a kan soyayyarsu ga dukiyoyinsu. Yayin da suka haƙura da abin da ransu yake so, suka fitar da dukiyarsu suka bayar don Allah; to zukatansu za su tsarkaka daga cutar rowa da bautar dukiya. | |||
# Abin da yake shiga rai sosai shi ne mutum ba ya son rabuwa da shi, don haka bayar da shi sadaka yana nuna karfin imanin mai yin hakan. | |||
# Yayin da mawadata za su rika bayar da dukiyarsu da suke so ga talakawa, wannan zai kawo gyaruwar al'umma, kuma ya kara dankon zumunta tsakanin mawadata da talakawa marasa abin hannu, sai rayuwa ta yi kyau ga kowa da kowa. | |||
# Yin sadaka don Allah, domin Allah ya san komai da ke cikin zukatan bayinsa, kuma zai yi musu sakayya gwargwadon abin da suka kudurce na ikhlasi ko hashinsa. | |||
# Allah ya neme mu da mu ciyar da wani abu na dukiyarmu wanda muke so, ba duka ba. Wannan yana daga cikin rahamar Allah da tausayinsa ga bayinsa, wajen dora musu abin da za su iya dauka, ba wanda zai gagare su ba. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 93-94 == | |||
# Duk wani abinci ya kasance halal ne ga Banu Israila sai abin da shi Isra'ilu ya haramta wa kansa tun kafin a saukar da Attaura. Ka ce: "To ku zo da Attaura, sai ku karanta ta in kun kasance masu gaskiya. | |||
# To duk wanda ya kirkiri karya ya jingina wa Allah bayan wannan, to wadannan su ne azzalumai. | |||
Allah a wadannan ayoyi yana ba da labarin cewa, kafin a saukar da Attaura ga Annabi Musa, duka wani nau'i na abinci halal ne ga Banu Isra'ila su ci, sai nau'i guda ɗaya wanda shi Isra'ilu, wato Annabi Yaqoob ya haramta wa kansa, ba Allah ne ya haramta masa ba, sannan daga baya 'ya'yansa su ma suka yi koyi da shi, suka haramta wa kawunansu cin wannan nau'i na abinci. Wannan kuwa shi ne naman rakuma da nononsu. To bayan saukar da Attaura, sai Allah ya haramta musu abin da ya ga dama a cikinta, ya kuma halatta musu abin da ya ga dama. Don haka wannan hukuncin ya shafe wancan hukunci na halatta musu komai, sai rakuma da nononsu. Sai Allah Ta'ala ya umarci Annabinsa da ya nemi Yahudawa su dauko littafin Attaura su karanta idan abin da suke fada gaskiya ne, wanda kuma ba za su gan shi ba. To bayan Allah ya tsayar musu da hujja, sai ya fada musu cewa, duk wanda ya kuskura ya yi masa karya bayan wannan bayanin da suka ji; to wadannan su ne azzalumai. | |||
Abdullahi bin Abbas yana cewa: Wata kungiyar Yahudawa sun je gaban Annabi suka ce: "Ya Baban Alqasim, za mu tambaye ka wasu abubuwa, ka ba mu amsarsu, domin babu wanda ya san su sai annabi." | |||
Daga cikin abin da suka tambaye shi, sun ce: | |||
"Wane abinci ne Isra'ilu (Jacob) ya haramta wa kansa tun kafin a saukar da Attaura?" | |||
“What did Jacob forbid himself of food?” | |||
Sai Annabi ya ce: "Na hada ku da Allah, shin kun san cewa, Isra'ilu (Annabi Yaqoob/Jacob) ya dade yana rashin lafiya mai tsanani, sai ya yi bakance na cewa, idan Allah ya ba shi lafiya to zai haramta wa kansa abin shan da ya fi so da abincin da ya fi so, kuma abincin da ya fi so shi ne naman rakuma. Abin shan da ya fi so kuma shi ne nononsu?" | |||
Sai Yahudawan nan suka ce: "Gaskiya ne, haka ne." [Ahmad #2471 da Tafsirin Tabari #7420, da Almu'ujamaul Kabir 12:246 #13012]. | |||
; 3.93 Abbas - Tanwîr al-Miqbâs min Tafsîr Ibn ‘Abbâs | |||
: (All food was lawful unto the Children of Israel) all food that is lawful for Muhammad and his community today was lawful for the Children of Israel, the sons of Jacob, (save that which Israel) Jacob (forbade himself) by the way of vows, ((in days) before the Torah was revealed) before the revelation of the Torah to Moses, Jacob forbade himself the meat and milk of camels. When this verse was revealed, the Prophet (pbuh) asked the Jews: “What did Jacob forbid himself of food?” They said: “he did not forbid himself any type of food, and whatever is forbidden for us today, such as the meat of camels and other things, was already forbidden on all prophets, from Adam to Moses (pbut). It is only you who make such things lawful”. And they claimed those things were also forbidden in the Torah. Hence Allah said to Muhammad (pbuh): (Say) to them: (Produce the Torah and read it (unto us)) where they are made forbidden (if ye are truthful) in your claim. But they failed to produce the Torah and knew they were liars since there was nothing in the Torah to substantiate their claim. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Martani ga Yahudawa masu karyata samuwar shafe hukunci a sharia, wato naskhu. | |||
# Umartar su da su dauko Littafin Attaura su karanta, wata hanya ce ta kafa wa abokin husuma hujja da abin da ya yi imani da shi kuma ya yarda da shi, wadda ba ta yadda zai iya kauce mata. | |||
#Umartar su da cewa su karanta su da kansu, bai ce 'mu karanta' ba, domin idan da Musulmi ne za su karanta, suna iya cewa ba su yarda ba, su rika tuhumar Musulmi cewa sun yi kari ko ragi a cikin karatun. Don haka su suka karanta da kansu, suka kuma ga gaskiyar a fili. | |||
#Kira zuwa ga bin gaskiya, domin duk sa'adda gaskiya ta bayyana a fili, kuma mutum ya kauce mata; to wannan ya tabbata babban azzalumi. Domin babu zaluncin da ya kai a kirawo shi zuwa ga hukunci da Littafin Allah, sannan ya bijire, saboda girman kai da kangara. | |||
#Mayar da martani ga Yahudawa masu da'awar suna bin addinin Annabi Ibrahimu, amma kuma suna jayayya da Musulmi a kan an halatta musu wasu abubuwa da su aka haramta musu a cikin Littafin Attaura. Domin ai addinin Annabi Ibrahimu bai haramta abubuwan da su aka haramta musu su a cikin Attaura ba. Don haka Musulmi su ne masu bin Addinin Annabi Ibrahimu na gaskiya. | |||
== Tarjama da Tafsirin Aya Ta 95-97 == | |||
# Ka ce: "Allah Ya yi gaskiya. Don haka ku bi addinin Ibrahimu, mai karkace wa barna, kuma bai taba zama daya daga cikin mushirikai ba." --Quran/3/95 | |||
# Lalle farkon daki da aka tanada don mutane (su yi ibada a cikinsa) shi ne wanda yake cikin Bakka, (daki ne) mai albarka, kuma shiriya ne ga talikai. --Quran/3/96 | |||
# A cikinsa akwai ayoyi bayyanannu, (kuma akwai) Maqamu Ibrahim; wanda duk ya shige shi ya zama amintacce. Kuma lalle Allah Ya wajabta wa mutane ziyarar wannan dakin ga wanda ya sami iko. Wanda kuwa ya kafirce, to lalle Allah Mawadaci ne ga barin talikai. --Quran/3/97 | |||
A wadannan ayoyi, Allah yana umartar Annabi SAW da ya ce wa Yahudawa, duk abin da Allah ya labarta ko ya shar'anta na hukuncil to gaskiya ne, kamar abin da ya fada musu cewa, babu wani abin da Allah ya haramta musu kafin saukar da Attaura, sai nau'i biyu (2), watau naman rakumi da nonansa. Don haka su zo su bi addinin Annabi Ibrahimu Alaihissalam, idan har su masu gaskiya ne game da tutiyar su ta cewa su jikokinsa ne' domin shi mai kadaita Allah ne, ba ya shirka, ba ya kuma tare da masu yin ta. | |||
Sannan Allah ya ba da labarin cewa, farkon dakin da aka gina shi domin mutane su bauta masa a cikinsa, kuma su yi ɗawafi su yi salla, su yi i'itikafi shi ne Ɗakin Ka'aba. Ɗakin Allah ne mai alfarma da ke garin Makka, mai ɗimbin albarka da abubuwan amfani masu yawa, na addini da na rayuwa, kamar riɓanyar lada a wurinsa da kuma arziki mai ɗimbin yawa da Allah ya kawo a garin, kuma shiriya ne ga ɗaukacin talikai, musamman zamantowarsa alƙibla ga Musulmi baki daya lokutan sallolinsu. Kuma shi ne wurin hajjinsu da umurarsu. To amma Yahudawa da Nasara masu tutiyar su ne a kan addinin Annabi Ibrahim Alaihissalam, sai ga shi ba sa zuwa Dakin da ya gina domin aikin hajji da umara, wanda hakan yake nuna sun yi [[hannun riga]] da shi, ba su da addininsa. | |||
An karbo daga Abu Zarri ya ce: Na tambayi Manzon Allah SAW cewa wane masallaci aka fara [[ginawa]] a bayan ƙasa? | |||
I heard Abu Dharr saying: I asked the Messenger of Allah (ﷺ) about the mosque that was first [[set up]] on the earth. | |||
Sai ya ce: Masallaci mai alfarma. | |||
He said: Masjid Harim. | |||
''Sai na ce: "Sai kuma wanne?" Sai ya ce: "Masallacin Qudus."''<br>I said: Then which next? He said: The Masjid al-Aqsa. | |||
Sai na ce: "Shekaru nawa ne a tsakaninsu?" | |||
I said: How long is the space of time between the two? | |||
Sai ya ce: "Shekaru arba'in (40). Sannan duk inda salla ta kama ka bayan haka; to ka fuskance shi a sallarka, a nan falalar take." [Bukhari #3366 da Muslim #520] | |||
He said: Forty years. He (then) further said: The earth is a mosque for you, so wherever you are at the time of prayer, pray there. https://sunnah.com/muslim:520b | |||
A cikin wannan Dakin akwai dalilai bayyanannu masu nuna kadaitakar Allah da hikimarsa da adalcinsa da girman Qudirarsa da sauran siffofinsa madaukaka, da kuma wasu alamomi masu nuna girman darajar wannan Dakin, daga cikinsu har da wuraren da Annabi Ibrahim ya tsaya domin aikin hajji, kuma duk wanda ya shiga cikinsa; to ya aminta daga duk wani abin ƙi. Allah ya farlanta zuwa wannan Daki domin gabatar da aikin hajji ga duk wanda Allah ya ba shi iko, na lafiya da guziri da abin hawa. Amma duk wanda ya karyata hajji ko ya bijire, to ya sani Allah mawadaci ne, ba ya bukatar hajjinsa, ba ya ma da bukata a wurin dukkan talikai. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Dakin Ka'aba shi ne farkon daki da Allah ya tannade shi a bayan kasa don ibada. Don haka wajibi ne a kan kowane Musulmi ya girmama shi. | |||
#Wajibi ne a kan kowane Musulmi da Allah ya hore masa damar zuwa hajji, ya gaggauta zuwa, kada ya yi jinkiri. | |||
#Allah cikakken mawadaci ne, ba shi da bukatar komai a wurin halittunsa, amma duk halittunsa mabukata ne a wajensa. | |||
#Allah ba ya farlanta wa bayinsa abin da ya fi karfinsu. Duk wani umarni ko hani da Allah zai nemi bawansa da shi to sai idan ya san yana da iko a kansa, idan ba shi da iko; to ya fadi daga kansa. | |||
Tarjama da Tafsirin Aya Ta 98-99 | |||
# Ka ce: "Ya ku Ma'abota Littafi, don me kuke kafirce wa ayoyin Allah, kuma Allah Mai ba da shaida ne ga abin da kuke aikatawa?" --Quran/3/98 | |||
# Ka ce: "Ya ku Ma'abota Littafi, don me kuke kange wanda ya yi imani ga hanyar Allah, kuna son ta zamo karkatacciya, kuma ku da kanku masu shaida ne, kuma Allah ba gafalalle ne game da abin da kuke aikatawa ba?" --Quran/3/99 | |||
A wadannan ayoyi Allah yana umartar Annabinsa da ya tambayi Yahudawa da Nasara, me ya sa suke musanta hujjojin da Allah ya saukar da su a littattafansu masu dauke da tabbatar da gaskiyar annabcin Annabi da gaskiyar abin da ya zo da shi, tare da sun san cewa babu wani aikinsu da zai buya a wurin Allah? Allah yana ganin duk irin ayyukan da suke yi. | |||
Kuma ya umarce shi da ya kara tambayar Yahudawa, me ya sa suke kokarin batar da muminai daga kan hanyar Allah, suke kuma kokarin su ga wannan hanyar ta gaskiya ta karkace, alhalin sun san gaskiyar, kuma sun san munin abin da suke aikatawa? To su sani Allah ba rafkananne ne game da abin da suke aikatawa ba, yana sane da komai, kuma duk zai yi musu hisabi a kai ranar Alqiyama. | |||
'''Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:''' | |||
# Fito da hakikanin su wane ne Ma'abota Littafi da fito da siffofinsu a fili a gane su. Suna nuna su masu riko da addini ne, alhalin karya suke, sun riga sun kafirce wa wani abu daga littafin Allah na Alkur'ani. Wanda duk ya kafirce wa wani abu daga littafin Allah; to ya kafirce wa littafin ne gaba dayansa. Da a ce sun yi imani da abin da ya zo a cikin littafinsu, to da sun yi imani da duk wani annabi da aka aiko bayan annabinsu. Domin addini a hakikaninsa guda daya ne, wanda duk ya fahimci addinin gaskiya; to duk wani addini da ya zo daga Allah, zai fahimce shi ya karbe shi. | |||
# Fadar cewa Allah yana ganin duk abin da suke aikatawa, kuma shi ba rafkananne ne game da ayyukansu ba, wannan shi zai razana ya firgita duk wani mayaudarin mutum, kafiri, batacce mai batarwa. | |||
# Hanyar Allah mikakkiya ce [[ɗoɗar]], ba ta da wata karkata ko kadan; duk kuma wata hanya wadda ba ta Allah ba; to karkatacciya ce. | |||
# Allah ya zargi masu kange wanda ya yi imani su hana shi bin hanyar gaskiya, tare da cewa sun hana kafirai ma bin gaskiyar, domin karkatar da mumini daga Musulunci zuwa ga kafirci ya fi muni fiye da karkatar da kafiri, domin da ma shi a karkace yake, sabanin mumini wanda shi raba shi da gaskiya aka yi, aka ingiza shi cikin kafirci; wannan kuwa ya fi muni a wurin Allah. | |||
[[Category:Quran/3]] | [[Category:Quran/3]] |