Toggle menu
24K
663
183
158.1K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Line 400: Line 400:
Never a Prophet had been sent before me by Allah towards his nation who had not among his people (his) [[disciples]] and [[companions]] who followed his ways and obeyed his command... [https://sunnah.com/muslim:50]
Never a Prophet had been sent before me by Allah towards his nation who had not among his people (his) [[disciples]] and [[companions]] who followed his ways and obeyed his command... [https://sunnah.com/muslim:50]


Allah kuma sai ya ba da labarin irin makircin da Banu Isra'ila suka ƙulla ga Annabi Isa, na ƙoƙaron hallaka shi. Su suna ƙulla makircinsu, Allah kuma yana shirya musu martani a kan mafi ƙarfi, mafi sani.
Allah kuma sai ya ba da labarin irin makircin da Banu Isra'ila suka ƙulla ga Annabi Isa, na ƙoƙaron hallaka shi. Su suna ƙulla makircinsu, Allah kuma yana shirya musu martani a kan mafi ƙarfi, mafi sani. Don haka sai Allah ya jefa kamannin Annabi Isa a kan daya daga cikinsu, sai suka kama shi suka kashe shi, suna zaton Annabi Isa ne suka kashe. Shi kuma Allah ya jefa masa barci, sannan ya dauke shi zuwa sama. Allah ya fada game da Annabi Isa cewa, zai karbi ransa irin karbar ran mai barci, yana Sannan zai daukaka shi zuwa gare shi da gangar jikinsa da kuma ruhinsa, sannan zai kubutar da shi daga wadanda suka kafirta, ya fitar da shi, ya daga shi zuwa sama, sannan zai sanya mabiyansa su zama su ne masu rinjaye a kan kafirai da karfin hujja da izza da daukaka har zuwa tashin alkiyama. Wadannan mabiyan nasa da Allah yake yi wa wannan alkawari, su ne Nasara, wadanda suka tsaya daidai a kan koyarwarsa har zuwa lokacin aiko Annabi Muhammad, sai kuma Musulmi wadanda su ne mabiya na gaskiya ga Annabi Isa, wadanda Allah ya karfafe su, ya ba su nasara a kan Yahudawa da Nasara da sauran kafirai.
 
Sai kuma Allah ya fada wa masu sabani cikin lamarin Annabi Isa cewa, dukkansu makomarsu zuwa gare shi take, kuma zai yi hukunci a tsakaninsu game da wannan sabani da suke yi. Hukuncinsa kuwa shi ne, zai yi musu azaba mai tsanani a nan duniya, ta hanyar kisa da dauri da kaskanci da wulakanci da raba su da dukiyoyinsu da kuncin zukata da za su yi ta fama da shi, sannan kuma a lahira su gamu da azabar Jahannama, a lokacin da babu wanda zai taimaka musu, ya kare su daga azabar Allah. Su kuma wadanda suka yi imani, kuma suka yi aiki na kwarai, hukuncinsa a kansu shi ne, zai cika musu ladansu babu ragi ko tawaya a duniya da lahira. A nan duniya ta hanyar ba su nasara kan abokan gabarsu, da izza da rayuwa mai kyau da kyakkyawan ambato da sauransu, a lahira kuwa ya saka musu da gidan Aljanna cikin ni'ima ta har abada. Kuma Allah ba ya son azzalumai, don haka shi kansa babu yadda za a yi ya yi zalunci cikin hukuncinsa.  


[[Category:Quran/3]]
[[Category:Quran/3]]