Toggle menu
24K
665
183
158.2K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations

Tafsirin ayoyin 1-5 na Surar Ali Imran

Allah ya bude wannan Sura da harrufa kamar yadda ya yi a Baqara, domin bayanin mu'ujizar Alƙur'ani, don nuna babu mai iya kawo kamarsa, duk kuwa da cewa magana ce da ta kunshi haruffa na Larabawa irin wadanda suke rubutu da su. Sannan Allah ya yi bayanin Allantakarsa da cewa, shi ne abin bauta na gaskiya, wanda daga cikin siffofinsa, shi ne Rayayye, mai cikakkiyar rayuwa, wadda ta siffantu da dukkan siffofi na kamala, Tsayayye da Zatinsa, ba shi da bukata a wurin wani cikin halittarsa, kuma shi ne mai tsayawa da taimakon kowa da komai, don haka kowa yana da bukata a wurinsa. Daga cikin taimakonsa da rahamarsa ga bayinsa, shi ne ya aiko musu da Annabi SAW, ya kuma saukar masa da Alkur'ani, wanda yake cike da gaskiya, kuma yake gaskata littattafan da suka gabace shi. Kuma Allah ya saukar da Attaura ga Annabi Musa (alaihissalam) da Linjila ga Annabi Isa (aS) tun kafin saukar da Alkur'ani. Allah ya saukar da littattafan nan ne dukkansu saboda shiriyar da mutane. A cikinsu Allah ya saukar da bin da yake bambancewa tsakanin ƙarya da gaskiya da tsakanin shiriya da ɓata, saboda haka Allah ya yi alkawarin azaba mai tsanani ga wadanda suka kafirce wa ayoyinsa a ranar gobe kiyama. Allah SWT babu wanda zai iya rinjayar sa, kuma babu abin da zai gagare shi, kuma shi mai gaggawar daukar fansa ne ga wanda ya saba masa.


Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Kasancewar dalilin saukar ayoyin farko na wanna Sura shi ne jayayyar da Nasaran Najrana suka yi da Annabi SAW dangane da sha'anin Annabi Isa (aS), sai ya zamana ya dace a bude wannan Sura da wadannan haruffa, wadanda suke ishara zuwa ga kalubalantar masu karyata Alkur'ani.
  2. Faɗar Allah SWT cewa: "Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai shi..." mayar da martani ne ga Nasara masu cewa Annabi Isa (aS) Allah ne.
  3. Siffofin nan na Allah guda biyu, (Rayayye da Tsayayye da Zatinsa) hada su wuri guda yana nuna siffantuwar Allah da dukkan siffofi na kamala. 'Rayayye' yana nufin kamalar siffofinsa duka, 'Tsayayye da Zatinsa' yana nufin kamalar ayyukansa gaba daya, don haka sun kunshi kamalar Zati, da kamalar ayyuka.
  4. Attaura da Linjila shiriya ne ga mutane a lokacinsu, amma bayan saukar da Alkur'ani, babu wata shiriya da ta rage sai ta Alkur'ani kadai.
  5. Musulunci shi ne addinin gaskiya, wanda ya hada bautar Allah shi kadai da kuma imani da annabawan Allah gaba daya.

Tarjama da Tafsirin aya 5-9

A wadannan ayoyin, Allah yana bayanin gamammen iliminsa, wanda ya kewaye komai, don babu wani abu da yake ɓuya a gare shi, a sama yake ko a ƙasa. Shi ne yake halittar ku bisa kamanni daban-daban a cikin iyayenku yadda ya ga dama, don haka shi ne kadai ya cancanta a bauta wa; ba shi da wani abokin tarayya. Shi ne Mabuwayi a cikin mulkinsa; ba mai iya ja da shi ko ya fi karfinsa, kuma shi mai hikima ne a cikin ayyukansa da shari'unsa, babu wani tasgaro a cikinsu ko kadan. Shi ne wanda ya saukar wa wannan Annabi Alkur'ani, wanda ya kunshi ayoyin da suke a fili, ma'anoninsu a bayyane suke, babu wani abu mai rikitarwa tare da su, ma'anoninsu a bayyane suke, babu wani abu mai rikitarwa tare da su, su ne kuma tushen wannan littafi, kuma su ne mafiya yawa a cikinsa. A cikinsa kuma akwai wadansu ayoyi wadanda ma'anarsu take da rikitarwa ga wasu mutane. To amma sai a samu wadansu karkatattun mutane masu cutar kauce wa gaskiya a zukatansu, suna bibiyar wadannan ayoyi masu rikitarwa, suna barin ayoyin da ma'anoninsu suke a fili, ba don su sami wani abu da za su kafa hujja da shi a kan soye-soyen zukatansu. Su kuwa wadannan ayoyi masu rikitarwa, babu wanda ya san hakikanin fassararsu sai Allah. Malamai masu zurfin ilimi na Alkur'ani su ma sukan san tafsirin ma'anonin ayoyin, amma ba za su iya sanin hakikanin al'amarin ba, da yadda karshen zai kasance, domin wannan Allah ne kadai ya san shi. Malamai masu zurfin ilimi sukan shelanta imaninsu da wadannan ayoyi masu rikitarwa. Duk kuma ayoyin na Alkur'ani daga Allah ne, amma ba kowa ne yake wa'azantuwa ba sai masu lafiyayyen hankali.

An karbo daga A'isha (rA) ta ce: "Annabi SAW ya karanta wannan ayar, sai ya ce: "Idan kika ga wadanda suke bibiyar ayoyi masu rikitarwa a cikin Alkur'ani; to su ne wadanda Allah ya ambata, don haka ki guje su." (When you see such verses, avoid them, for it is they whom Allah has pointed out (in the mentioned verses)[1]).

Malamai masu zurfin ilimi addu'a suke yi ko da yaushe, suna rokon Allah kada ya karkatar da zukatansu su saki shiriya bayan Allah ya shiryar da su, ya yi musu rahama, ya kara m usu imani da tsayuwa a kan gaskiya, domin Allah shi ne mai yawan kyauta da ihsani ga bayinsa. Kuma suna addu'a suna cewa:

"Ya Allah, kai ne za ka tara mutane a rana Alkiyama, ranar da babu shakka a zuwanta, domin yin hukunci da sakayya ga kowa a kan aikinsa, don haka ka gafarta mana a wannan ranar, ka yi mana afuwa."

Sun kuma yi Imani da cewa, lalle Allah ba ya saba alkawarinsa na cewa, wanda duk ya yi imani da shi, ya bi Manzonsa; to zai gafarta masa.

An karbo daga Abdullahi dan Amru ya ce, Annabi SAW ya ce:

Abdullah b. Amr b. al-'As reported that he heard Allah's Messenger (ﷺ) as saying:

"Lalle zukatan 'yan'adam duka suna tsakanin yatsu biyu ne

Verily, the hearts of all the sons of Adam are between the two fingers


daga yatsun Allah Mai rahama, tamkar zuciya daya,

out of the fingers of the Compassionate Lord as one heart.


yana sarrafa su yadda ya ga dama."

He turns that to any (direction) He likes.


Sannan sai Annabi SAW ya yi addu'a yana cewa: "Ya Allah Mai sarrafa zukata, ka sarrafa zukatanmu a kan da'arka."

Then Allahs Messenger (ﷺ) said: O Allah, the Turner of the hearts, turn our hearts to Thine obedience. [2]


Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Jan hankalin dan'adam a kan ya kyautata halayensa, da ayyukasa, domin Allah Mahaliccinsa yana ganin sa, babu abin da yake ɓuya a gare shi.
  2. Yana daga cikin alamomin karkacewar zuciya, bibiyar ayoyin Alkur'ani masu rikitarwa, don mutum ya saka kansa ko wasu cikin shakka.
  3. Idan mai karatu ya yi wakafi a daidai (illallahu) to hakan yana nuna a cikin Alkur'ani akwai abin da babu wanda ya san fassararsa sai Allah. Fassara a nan, ko kuma 'tawili', kamar yadda ya zo a ayar, ana nufin karshen al'amari, ko kuma yadda hakikanin al'amarin zai kasance. A nan akwai jarrabawa da Allah yake yi wa bayinsa game da abubuwan da ba za su iya fahintar su da tsurar hankalinsu ba. Shin za su ce sai sun gano su ta haka, ko kuwa za su sallama wa Allah SWT su tsaya a matsayinsu?
  4. Babu