Sheikh Khalid in the sermon flayed the government over its failure to tame the escalating insecurity and killings in the country.
In the sermon, the imam hinted at some measures that electorate should devise should the authorities fail to protect their lives.
He said, “Nigerian masses should resort to only one term which is – protect our lives, we will come out to vote; let us be killed, we will not come out to vote, since it’s only elections that you people know,” he added.
In a statement, the chairman of the mosque committee, Senator Saidu Muhammed Dansadau sent to BBC Hausa Service, said the committee suspended the embattled imam over his sermon that it deemed ‘inciting public outrage’.
The statement read, “I am informing you that you have been suspended from leading prayers in the Apo Legislative Quarters Mosque from today being April 2nd, 2022 until further notice.
“The decision was taken out of the inciting Friday sermon you delivered on April 1st, 2022; where you advised people not to vote come 2023 general elections unless politicians respond to some critical questions.
“You should have advised them to vote out those that transgress the Almighty and breach people’s social contract as well as the state.”
The committee maintained that Sheikh Khalid sermon negated tenets of Islam.
The committee has immediately appointed Malam Mohammad who will deliver Ramadan Tafsir while Malam Abdullahi will be leading Friday prayers.
However there’s no reaction from the suspended imam.
Sheikh Khalid has been an avid critic of the government over the escalation of insecurity in Nigeria.
His latest sermon is coming a couple of days following terrorists’ devastating attack on Kaduna-bound train where a yet-to-be ascertained number of passengers were killed and others abducted.
Sheikh Nuru Khalid a cikin hudubarsa ta ranar Juma'a 1 ga watan Afrilu, ya caccaki gwamnati kan kasa magance matsalar tsaro da kuma yawaitar kashe-kashe a Najeriya.
A cikin hudubar, malamin ya faɗi matakin da ya kamata talakawa su ɗauka idan har gwamnati ta bari aka ci gaba da kashe su, na kin fitowa zaɓe.
"Sharadin talakan Najeriya ya zama guda ɗaya kawai, ku hana kashe mu, mu fito zabe, ku bari a kashe mu, ba za mu fito zaɓe ba, tun da ku ba abin da kuka sani sai zabe," in ji Sheikh Nuru Khalid a huɗubarsa.
A cikin wani saƙo da shugaban kwamitin Masallacin Sanata Saidu Muhammed Dansadau ya aika wa BBC, ya ce sun dakatar da Malamin daga yin limanci saboda hudubar malamin da kwamitin ya kira ta tunzura jama'a.
Sanarwar ta ce: "Ina mai sanar da kai cewa an dakatar da kai daga Limamanci a Masallacin ƴan Majalisar da ke shiyyar Apo Abuja daga yau 2/4/22 har zuwa wani lokaci."
"An ɗauki wannan matakin ne saboda hudubar Juma'a ta tunzurawa a ranar 1/4/22 inda ka ba mutane shawarar kada su yi zaɓe a 2023 har sai 'yan siyasa sun amsa wasu tambayoyi."
Sanarwar ta ƙara da cewa "ya kamata a ce ka ba su shawara su fito zaɓe don kawar da waɗanda suka saɓa wa Allah, da masu zaɓe da kuma ƙasa."
Kwamitin ya ce hudubar Sheikh Nuru Khalid ta saɓa wa addinin Islama. Kuma a cikin sanarwar kwamitin ya naɗa sabbin lamamai na Masallacin inda Malam Mohammad zai yi tafsiri, yayin da kuma Malam Abdullahi zai jagoranci Juma'a.
Babu wani martani daga Sheikh Nuru Khalid game da matakin da kwamitin ya ɗauka na dakatar da shi, kuma BBC ta yi ƙoƙarin tuntuɓar malamin amma wayarsa a kashe.
Sheikh Nuru Khalid ya sha caccakar gwamnati kan tabarbarewar tsaro a Najeriya, kuma hudubarsa na zuwa ne bayan harin da ƴan bindiga suka kai wa jirgin ƙasa a ranar Litinin inda aka kashe mutum takwas tare da sace mutane da dama.
A cikin huɗubar Malamin ya ambaci wani da ke cewa "harakar tsaro ta zama kasuwanci a Najeriya, jinin talaka ya zama kayan kamfen a kasar nan, sai zaɓe ya kusa kashe kashe zai karu."
"Mun dade muna hakuri - hanya ba kyau, talauci mun hakura, tsadar rayuwa mun hakura, karya mun hakura, kwashe kudin kasa mun hakura, ku bar mu mu zauna da ranmu kuma ba zai yiyu ba?"
Don haka a cewar Malamin abin da ya kamata talakan Najeriya ya yi shi ne ya ƙauracewa zaɓe har sai an daina kashe rayukan al'umma.