#
|
Hadith 2
|
Hadisi na biyu
|
1
|
Also on the authority of `Umar (radi Allaahu ‘anhu), who said:
|
An ruwaito daga Umar Allah ya yarda da shi yace:
|
2
|
One day while we were sitting with the Messenger of Allaah ﷺََ there appeared before us a man whose clothes were exceedingly white and whose hair was exceedingly black;
|
Wata rana muna wurin Manzon Allah ﷺََ, Sai wani mutum ya zo mana mai tsananin farin tufafi kuma mai tsananin baqin gashi;
|
3
|
no signs of journey were to be seen on him and none of us knew him. He walked up and sat down in front of the Prophet ﷺََ,
|
babu wata alamar tafiya a tattare da shi, har ya zauna kusa da Annabi ﷺََ.
|
4
|
with his knees touching against the Prophet’s ﷺََ and placing the palms of his hands on his thighs he said:
|
Sai ya jingina guiwoyinsa zuwa guiwoyinsa, ya kuma ɗora tafukansa akan cinyoyinsa, yace:
|
5
|
“O Muhammad, tell me about Islam.
|
Ya Muhammadu ﷺََ , bani labari akan Musulunci?
|
6
|
The Messenger of Allaah ﷺََ said: Islaam is to testify that there is no deity worthy of worship but Allaah and Muhammad is the Messenger of Allaah,
|
manzon allah ﷺََ Yace :Ka shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma annabi Muhammadu manzon Allah ne,
|
7
|
to perform prayers, to give zakaah, to fast in Ramadaan, and to make the pilgrimage to the House if you are able to do so.
|
kuma ka tsayar da salla, kuma ka bada zakka, kuma ka yi azumin watan ramadana, kuma ka yi hajjin ɗaki; idan ka samu hanyar zuwa gare shi.
|
8
|
He said: “You have spoken rightly”; and we were amazed at him asking him and saying that he had spoken rightly. He (the man) said: “Tell me about Eemaan.
|
Sai yace: ka yi gaskiya Sai muka yi mamakinsa yana tambayarsa kuma yana gaskata shi! Sai yace: ka bani labari akan imani?
|
9
|
He (the Prophet, ﷺََ ) said: “It is to believe in Allaah, His Angels, His Books, His Messengers, and the Last Day, and to believe in divine destiny (qadr), both the good and the evil of it.
|
Yace: Ka yi Imani da Allah da Mala’ikunsa da littatafansa da Manzanninsa da ranar ƙarshe, kuma ka yi imani da qaddara na alkhairinsa da na sharrinsa.
|
10
|
He said: “You have spoken rightly.” He (the man) said: “Then tell me about Ihsaan.”
|
Yace: Kayi gaskiya. Yace: To ka bani labari akan “ihsani”?
|
11
|
He (the Prophet, ﷺََ ) said: “It is to worship Allaah as though you see Him, and if you do not see Him, then (knowing that) truly He sees you.”
|
Sai yace: Shine ka bauta wa Allah kamar kana ganinsa, idan kai baka ganinsa to shi yana ganinka.
|
12
|
He said: “Then tell me about the Hour.” He said: “The one questioned about it knows no better than the questioner.”
|
Yace: To ka bani labari akan qiyamah? Sai yace: Wanda ake tambayarsa akanta bai fi wanda yayi tambayar sanin lokacinta ba.
|
13
|
He said: “Then tell me about its signs.”
|
Sai yace: To ka bani labara kan alamominta?
|
14
|
He said: “That the slave-girl will give birth to her mistress, and that you will see barefooted, naked destitute shepherds competing in constructing lofty buildings.”
|
Sai yace: Baiwa ta haifi uwar gijiyarta, kuma zaku ga marasa takalma tsiraru masu kiyon dabbobi suna yin gini masu tsayi.
|