Toggle menu
24.1K
670
183
158.7K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

hausaradio1

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Revision as of 23:21, 14 February 2019 by Admin (talk | contribs)

Kanun Labarai: HausaRadio.net's News Headlines Project using Anchor, Otter.ai, etc.

See also voa60
# Full Audio and Transcription of Hausa News Headlines
1

VOA Hausa Shirin Safe 0500 UTC (30:00) na 2017-8-31 [1], 2m 6s.

  1. Hosts: Ibrahim Ka-Almasih Garba, Ladan Ibrahim Ayawa.
  2. 1.1 Watanni bakwai da gwamnatin shugaba Trump ta fara aiki. <> 7 months of Trump administration.
  3. 1.2 Manufofin gwamnatin nasa game da harkokin ƙasashen waje sun fara bayyana. <> His foreign affair policies are starting to take shape.
  4. 1.3 A jiya Laraba ne, shugaba Donald Trump da sakataren tsaronsa, suka bada ra'ayin mabambanta akan yadda Amurka za ta tunƙari shirye-shiryen makami mai linzami da na nuclear na ƙasar Koriya ta Arewa / Koriya ta Arewa. <> National security and the North Korean nuclear threat.
  5. 2.1 Yanzu dai ana iya cewa mahaukaciyar guguwan nan biye da ambaliyan ruwa, ta yi sauƙi domin ko ta bar gab'an teku amma dai har yanzu tana da hatsari <> Hurricane Harvey starting to weaken/pass.
  6. 3.1 A yayin da ake haramar Babbar Sallah gobe, hukumomi sun fara d'aukar matakan ganin komai ya tafi daidai. Jami'an [ unintelligible ] da sojojin 'yan sanda da kuma jami'an hukumar tsaron farin kaya ta Civil Defense, inda ma suke kara da manyan tituna domin tabbatar da doka da oda. <> Eid preparations by organizations like Yan sanda and civil defense.
  7. 4.1 A yayin da a jihar Texas ta Amurka ake fama da bala'in ambaliyar ruwa da iska, wani ƙwararre a Nijeriya ya gargad'i ƙasashe masu tasowa.
  8. 5.1 Sannan sabon jakadan Nijeriya a Amurka, Muhammad Hassan, ya yi tsokaci kan ibar Nijeriya a idon duniya.
  9. 6.1 Kamar kowace ranar Alhamis, Grace Alheri Abdu na tafe da shirin Domin Iyali.
2

VOA Hausa Shirin Hantsi 0700 UTC na 2017-8-31 [2], 1m 12s.

  1. Hosts: Ibrahim Ka-Almasih Garba, Ladan Ibrahim Ayawa.
  2. 1.1 Cigaban hirar Aliyu Mustaphan Sokoto tare da sabon jakadan Nijeriya a Amurka Muhammad Hassan.
  3. 2.1 Kamar kowace ranar Alhamis, Usman Kabara na tafe da shirin sa na Nakasa ba Kasawa ba [3].
  4. 3.1 Relnuwalullah Muktar Abbas na tafe da sharhin jaridun k'asar Ghana.
  5. 4.1 Ra'ayoyin masu saurare.
3

BBC Hausa Shirin Hantsi 2019-2-4 (Mon Feb 4th) [4], 1m 12s.

  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. Sashen Hausa na BBC ku ka kama akan mita ashirin da ɗaya da ashirin da biyar da kuma mita talatin da ɗaya. Ko kuma a shafin mu na internet a BBCHausa.com da kuma manhajar TuneIn a BBC Hausa. Masu sauraro, Badriya Tijjani Kalarawi ke muku sallama a cikin shirin mu na hantsi.
4

DW Hausa Shirin safe 07.02.2019

A cikin shirin za a sha labaran duniya da kuma rahotanni kan zaben Najeriya da rikicin kasar Kamaru na 'yan aware da ke kara kamari. [5]

  1. Hosts: Ramatu Garba Baba
  2. Nigeria Elections 2019: Za mu duba yanda/yadda 'yan takara ke cigaba da bayyana hanyoyin da za su bi don ɓullowa mahimmam buƙatun al'ummar ƙasa. Ga kadan daga ra'ayoyin jama'an ƙasa kan abinda ya fi ci musu tuwo a ƙwarya[6]:
    1. Abubuwan da suka dawo yanzu tsakanin Zamfara da wani gefe na Katsina da gefe na Sokoto, shine yake wahalar da mu a Nigeria.
    2. Inda za'a shigo da fita Nigeria. <> Regarding Nigeria immigration / emigration.
  3. Cameroon: A Kamaru ma, matsalar tsaro ake fuskanta don kuwa rikici a tsakanin gwamnati da ɓangaren 'yan aware masu amfani da turancin Ingilishi ne ke ƙara ta'azzara.
5

BBC Hausa Shirin Rana 10am EST - BBC Hausa Thu Feb 7 [7]

  1. Hosts: Sulaiman Ibrahim Katsina
  2. Jiragen yaƙin Faransa sun kai sabbin hare-hare a Cadi (Chad) akan abinda suka ce. Wani ayari ne na 'yan bindiga ɗauke da manyan makamai. Wataƙila da [unintelligible] hamɓarar da gwamnatin Cadi.
  3. Tarayyar Turai ta ce masu sanya idanunta kan zaɓukan Najeriya za su je ƙasar, dukkuwa, da barazanar da gwamnan jihar Kaduna ya yi akan zuwan su.
    Ko ƙanƙani ba shi da nufin ya nemi a jima wani ko a hallaka wani ko ɗan Najeriya ko ɗan ƙasar waje dangane da harkar zaɓe. Magana ce yake yi da ta shafi kare kishin ƙasa da mutincin ƙasar sa ta Nigeria. --wakilin gwamnatin tarayya Garba Shehu
  4. Sojan Zimbabwe sun ce sun kammala aikin da suka yi na samar da kwanciyar hankali da bin doka a ƙasar.
  5. Za mu ji wani mataki da gwamnatin Amurka ta ɗauka akan Kamaru.
6

Pars Hausa Sunday, Feb 10th 2019 [8] [9]

  1. Hosts: Aminu Abdu
  2. Niger: The Minister of State for the Interior Mohamed Bazoum ya jagoranci wata tawaga da ta haɗa da 'yan majalisu da manyan jami'an ƙasar zuwa garin Adze* na cikin gwadomar Abalak da ke jihar Tahoua domin tattaunawa da al'ummar yankin kan abinda ya shafi harkokin tsaro da zaman lafiya na yankin.
  3. Nigeria: Rahotanni sun tabbatar da cewa wata gobara ta rutsa da wasu 'yan gudun hijira a sansanin Munguno, Borno. Za'a ji ra'ayin masana dangane da wannan lamari.
  4. Nigerians living in Cote D'voire: 'Yan Nijar da ke rayuwa a ƙasar Cote D'voire sun koka kan yadda suke samun matsala da katin ɗan ƙasa. Ganin cewa muhukuntan na Niger sun ƙi sabunta katin da ta yi daidai da zamani. Lamarin da ya sanya suke fuskantar matsala na gudanar da mu'amalarsu a ƙasar ta Cote D'voire.
  5. Morocco: Hukumomi a ƙasar Morocco sun sanar da janyewar ƙasar daga cikin gurundunar ƙawancen Saudiya a ƙasar Yemen tare da kiran jakadan ƙasar daga birnin Riyadh. Ko me hakan ya ke nufi, za mu ji ra'ayin masana.
  6. Shirin Ko Kun San da Tahir Amir Rajiyola*.
  7. Shiri na musamman (Special Report) dangane da zagayowar ranar nasarar juyin-juya halin Musulunci na Iran.
  8. Shiri na Matambayi Baya Ɓata da Muhammad Auwwal Bauchi.
7

BBC Hausa Shirin Yamma 09/02/2019 [10][11]

Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.

  1. Hosts: Ibrahim Mijinyawa
  2. Nigeria Elections 2019: Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP (the major opposition party), ta yi zargin cewa an hana ta gudanar da gangamin yaƙin neman zaɓe a Abuja.
    Har mun tura mutanen mu waɗanda za su je su shiya mana wurin tsayawa a yi magana (podium)... sai aka ce musu wannan wuri ba za a ba mu shi ba. Don haka sai dai mu nemi wani.
  3. Chad: Rundunar sojin Cadi kuwa, ta ce ta kama 'yan tawaye da dama da suka tsallaka cikin ƙasar daga kudancin Libya bayan artabun da aka yi da su a arewacin ƙasar.
  4. Ethiopia: Tsofaffin 'yan tawaye ne sama da dubu guda suka miƙa da makamansu bayan wata yarjejeniya da aka ƙulla da su da gwamnatin ƙasar.
8

BBC Hausa Shirin Safe 10/02/2019 [12] [13]

Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.

  1. Hosts: Umaymah Sani Abdulmumin
  2. Nigeria Elections 2019 / Zaɓe 2019: APC! APC! Today I want to teach Atiku a lesson.--Uban jam'iyyar APC Bola Ahmed Tunibu a yayin yaƙin neman zaɓen jihar Lagos ya ke cewa yau zan koyawa Atiku darasi. Za mu ji me yayi zafi da kuma yadda yaƙin neman zaɓen ya kasance.
  3. Sokoto Governor Debate: A yau BBC ke cika alƙawarinta na kawo muku mahawara tsakanin 'yan takaran gwamnan Sokoto.
  4. Africa: Shugwabannin ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Afrika za su soma wani taro da zai mayar da hankali wajen lalubo hanyoyin shawo kan matsalolin da suka addabi nahiyar su.
9

BBC Hausa Shirin Hantsi 10/02/2019 [14] [15]

Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.

  1. Hosts: Umaymah Sani Abdulmumin
  2. Turkey, China: Turkiyya ta buƙaci ƙasar Sin da ta gaggauta ta rufe sansanonin da take tsare musulmi 'yan ƙabilar Uyghur.
  3. UK: Yarima Philip na Birtaniya ya ajiye lasisinsa na tuƙi.
  4. Nigeria's corn farmers: Manoma masara sun bayyana irin yabon da suka ce sun samu a noman bara.
    Mun samu cigaba wajen bunƙasuwan masara daga shekara ta dubu biyar da sha biyar zuwa yanzu (2015-present). Da, masarar da ake nomawa a wannan lokaci ba ta wuce tonne miliyan sha biyar ba. Amma yanzu zuwa bana, noman da aka yi na bara shekara ta dubu biyu da sha takwas (2018), an noma ta miliyan ashirin.
  5. Shirin Mu Tattauna.
10

DW Hausa Shirin Safe 10.02.2019 [16] [17]

Za ku ji cewar kasar Turkiya tayi Allah wadai da irin cin zarafin da kabilar Uighur ke fuskanta a kasar Chaina

  1. Host: Zulaiha Abubakar Kibiya
  2. African Union: Ƙungiyar tarayyar Afika ta AU, za ta gudanar da babban taron ta na kwanaki biyu a birnin Adis Ababa na ƙasar Habasha (Ethiopia) inda shugwabannin ƙasashen Afrika za su tattauna batun kwararar baƙin haure daga nahiyar zuwa ƙasashen turai.
  3. Daidai lokacin da a cigaba da lalubo dabarun warware rikicin addini da ƙabilanci da ke barazana da rayuwar al'umar Filato.
  4. Cibiyar sasanta tsakanin addinai mai ofishi a Kaduna, ya ƙaddamar da shirin yafewa juna tsakanin al'ummomin jihar bayan shafe sama da shekaru goma sha bakwai ana tashin hankali.
  5. Shugaba Paul Kagame zai sauka daga muƙaminsa a ƙungiyar AU.
  6. An shawarci sojojin ƙasar Venezuela a kan kayan agaji.
  7. Turkiyya ta yi Allah-wadai da cin zarafin da ƙabilar Uighur ke fuskanta China.
11

VOA Hausa Shirin Rana 0500 UTC (30:00) na 2019-2-10 [18]

  1. Hosts: Zahara Aminu Fagge da Baba Yakubu Maƙeri
  2. Syria: Rundunar SDF ta k'asar Syria ta na samun goyon bayan Amurka, ta fatattaki 'yan k'ungiyar ISIS domin k'wace yankin k'arshe da ya rage a hannun k'ungiyar a gabashin Syria.
  3. South Korea: Amurka da Koriya ta Kudu a yau Lahadi sun sanya hannu a kan wata sabuwar yarjejeniya, wanda za ta k'ara kud'in da Seoul ke biyan Amurka na jibge sojoji a Koriya ta Kudu.
  4. Turkey: K'asar Turkiyya ta kira ga Cadi ta rufe wasu sansanoni da gidajen yari, inda ta kama 'yan Turkawa 'yan k'abilar Ogo miliyan d'aya. Wacce ta ayyana su abin kunya ga bil Adama.
12

RFI Hausa Labaran_16h00 na 2019-02-11 [19][20]


  1. Hosts: Azima Bashir Aminu
  2. UK: Rashin cimma yarjejeniyar ficewar Birtaniya daga EU, zai haddasa rasa guraban ayyukan yi dubu ɗari shida a sassan duniya.
  3. France: Zanga-zangar masu yaluwar riga a Faransa ta sanya shaku a zuk'atan masu zuba jari.
  4. Nigeria: Gobara ta cinye ofishin zab'e a Najeriya, daidai lokacin da ya rage kwanaki shida a gudanar da babban zab'en k'asar (source).
  5. Cameroon: A Kamaru, mayak'an 'yan aware, sun k'one wani asibiti tare da hallaka mutane hud'u.
13

BBC Hausa Yamma 11/02/2019 [21]

  1. Hosts: Sulaiman Ibrahim Katsina
  2. USA: Wakilan jam'iyyun demokurat da republican a Amurka suna ganawa a yau Litinin don ƙoƙarin cimma yarjejeniya a kan tsaron iyakar kasar don kauce ma a sake durk'usar ma ayyukan gwamnati.
  3. Kenya: Ana ta k'ara nuna damuwa a Kenya game da inda wata mai kare hakkin bil Adama take tun bayan da ta b'ata a ranar Laraba.
  4. Nigeria: Ana nuna fargaba gama da gobarar da tashi a ofisoshin hukumar zab'e na wasu k'ananan hukumomi.
    Abinda gobarar ta shafa a ofisoshin guda biyu na k'ananan hukumomi ɗin, ba fa zai yi wani illa a zab'en da ke gaba ba. Domin a halin dai yanzun, ba a kai ma kayan zab'e ofisoshin k'ananan hukumomi da su ke wadannan wurare ba.--INEC
  5. Nigeria: Rundunar 'yan sanda a Najeriya ta bayyana damuwa ne a kan k'aruwar ayyukan galatsi da d'aukar doka a hannu da wasu 'yan k'asar ke yi.

[22] [23]

14

Pars Hausa Tuesday, Feb 12th 2019 [24]


  1. Hosts: *Unintelligible - sounds like "Munshaba Adabu"
  2. Labaran duniya da rahotanni daga Niger da Ghana.
  3. China, Turkey: Za mu ji mahangar wasu ƙwararru akan abinda ke faruwa a ƙasar China na tsare da kuma killace musulmai kusan miliyan ɗaya da mahukuntan ƙasar suka yi tare kuma da kiran da ƙasar Turkiyya ta yi na ganin cewa an kawo ƙarshen wannan killacewar da aka yi musu.
  4. Nigerian Newspaper Headlines: Muna ɗauke da wasu daga kanun jaridun Najeria.
  5. Shirin Ko Kun San: Shirin kullun da ke bijiro da abubuwan da suka faru a tsawon tarihi.
  6. Labaran da suka faru a jamhuriyar musulunci ta Iran da nahiyar Africa a cikin mako guda.
  7. Shirin Duniyar Fasaha.

[25]

15

BBC Hausa Shirin Safe (Tue Feb 12th 2019 - 6:30am NG) [26]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. USA: 'Yan jam'iyyun Democrat da Republican, sun cimmawa matsayar kaucewa sake dakatar da ayyukan gwamnati a Amurka.
  3. Nigeria: Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyar PDP, ya ce rashin kayan aiki ne ke dawo da hannun agogo baya a yaƙi da ta'addanci a ƙasar.
    "I beleive our military are not getting the best of equipment... <> Na yi imani sojojin mu basa samun ingantattun kayan yaƙi. Wasu lokuta ma, za ka ga makaman da 'yan ta'adda ke amfani da su, sun fi na sojoji inganci da zamunanci."
  4. Election special: Sashen Hausa na BBC sun yi tanadi na musamman a lokacin zaɓen.
    "Saboda idan ka fara shiri, ba za ka tsaya ba, tun ƙarfe shida na safe (6 AM), har zuwa ƙarfe goma sha ɗaya na dare. Ɗanɗanon shirin da sauran shirin zai sauya, kamar yadda muka sauya shi a lokacin da muka yi bakukuwan cika shekaru sittin da kafuwa.

[27] [28]

16

BBC Hausa Shirin Hantsi (Tue Feb 12th 2019 - 7:30am NG) [29]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. India: 'Yan sanda Indiya sun ce mutane sha bakwai ne suka mutu, sakamakon wata gobara da ta tashi a wani otel da ke birnin Delhi.
  3. Haiti: Masu zanga-zanga sun yi ta ƙona tayoyi a titunan ƙasar Haite tare da jefan jami'an tsaro da duwatsu.
  4. Nigeria: Wasu 'yan Najeriya sun ce sun gaji da alƙawarin da gwamnati ke musu na bunƙasa harkar sufurin jirgin ƙasa a sassan ƙasar.
    "Muna jin daɗin yanda aikin kasancewa. Amma kuma abinda muke gude shine, kada yazo ya kasance kamar aikin bayan ya fara kuma a tsaya. Sabida, sun san abu kamar za su yi, za su yaudari mutane. Can kuma, su yi amfani da kuɗin su yi wani abu."
  5. Labarin wasanni <> sports.
  6. Nigeria Elections 2019: Za ku ji zargin da jam'iyyar APC da PDP ke yi kan kawowa juna hare-hare gabannin zaɓen da ke tafe a Najeriya.

[30]

17

BBC Hausa Shirin Rana (Tue Feb 12th 2019 - 3pm NG) [31]

  1. Hosts: Aminu Abdulkadir
  2. Spain: An soma wata muhimmiyar shari'a ta wani fitaccen d'an awaren yankin Catalonia a Madrid, babban birnin Spain.
  3. Nigeria: Wasu mata biyu 'yan yankin Ogoni a Najeriya, sun bayyana a wata kotu kan wata k'ara da aka shigar a k'asar Holland kan kamfanin mai na Shell.
  4. Nigeria 2019 Elections: A Najeriyar, yayin da ake k'aratar zab'e a k'asar, ko matasa za su yi wannan zab'e kuwa.
    1. "Zan yi zab'e inshaAllah. Kuma farkon lokaci na ne na yin zab'e a duniya. A zuciya na, ina tunanin zai yi amfani, inshaAllah."
    2. "Ban sama kati na ba. Na je in anshi kati na sai suka ce mun wai ba su yi printing d'in shi ba. Saboda haka, ina tunanin wannan karo ba zan samu in yi zab'e ba."

[32]

18

RFI Hausa Labaran_16h00 (Tue Feb 12th 2019 - 5pm NG) [33][34]


  1. Hosts: Muhammad Salisu Hamisu
  2. Spain: Jagororin masu kokarin b'allar da yankin Catalonia na k'asar Spain goma sha biyu, sun gurfana a gaban kotun k'olin k'asar a kotu a yau.
  3. France: Za'a ji cewa wasu mutane hud'u aka kama. Bayan haka kuma, hijirin bak'i na yawaita a Faransa.
  4. Africa: K'asashe sama da d'ari da ishirin da biyar (125) na gudanar da zaman taro a Addis Ababa, Ethiopia domin duba yadda aka yi a bincike cigaba da salwantar rayukan jama'a a duniya.
  5. Nigeria: A yau, a Lagos, d'an takarar jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya gabatar da taron gangamin yak'in neman zab'ensa.

[35]

19

VOA Hausa Shirin Rana 0500 UTC (Tue Feb 12th 2019) [36]


  1. Hosts: Sarfilu Hashim Gumel da Baba Yakubu Maƙeri
  2. USA: Masu tattaunawa a majalisun dokokin Amurka sun cimma babban yarjejeniya akan bada kud'ad'e na gudanar da ma'aikatun gwamnatin tarayya domin hana sake rufe gwamnatin a k'arshen wannan mako.
  3. India: Ak'alla mutane goma sha bakwai (17) sun mutu a yau Talata a cikin wani babban otel a birnin Delhi da sanyin safiyar yau.
  4. USA: Wata sabuwar 'yar majalisar dokokin Amurka, 'yar asalin Somalia da ta yi gudun hijira zuwa nan Amurka, ta nemi afuwa akan kalamai da ta yi na sukar lamirin yahudawa.

[37]

20

BBC Hausa Shirin Yamma (Tue Feb 12th 2019 - 8:30pm NGT) [38]


  1. Hosts: Aminu Abdulkadir
  2. Sudan: Jami'an tsaron ƙasar Sudan sun tsare wani rukunnin shegunnan malamai na jami'o'i. Da suka yi zanga-zangar ƙin jinin shugaba Umar Al-Bashir a Khartoum - babban birnin ƙasar.
  3. Nigeria: Rundunar 'yan sanda ta ce ta kama wasu mutane dangane da gobarar da tashi a wani ofishin hukumar zaɓe, yau a jihar Anambara. Gobarar ta haddasa ɓarna.
    "Toh, har yanzu dai ba mu kai ga tantance yawan adadin wannan na'uran, ko guda nawa ne suka ƙone ba. Amma dai sun kashe tamanin da biyar cikin ɗari (85/100) sun ƙone.
  4. DRC: 'Yan sanda sun tabbatar da kama mutane goma sha biyar dangane da rikicin ƙabilancin da ya haddasa mutuwar ɗarurwan mutane.
  5. Sports <> Labaran wasanni.

[39] [40] [41]

21

BBC Hausa Shirin Safe (Wed Feb 13th 2019 - 6:30am NGT) [42]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. Venezuela: Shugaban 'Yan adawa a Venezuela, ya sha alwashin shigar da kayan agaji. Duk kuwa da cewa shugaba Maduro ya ƙi amincewa da hakan.
  3. Nigeria: Ana cigaba da cece-kuce kan shugaba Muhammadu Buhari a jihar Zamfara. Da ake cewa hakan zai iya haddasa fitina. Toh sai dai kuma magoya bayanshi sun ce an yi masa mummunar fahimta.
  4. World Radio Day 2019: Shin kuma ko wace rawa ce rediyo ke takawa a rayuwar al'umma? Muna ɗauke da ƙarin bayani a cikin shirin. (20:51-24:41)[43][44][45]
  5. Sports: labarin wasanni.

[46] [47] [48]

22

BBC Hausa Shirin Hantsi (Wed Feb 13th 2019) [49]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. South Korea: Hukumomin Koriya ta Kudu, sun musunta iƙirarin shugaba Trump kan ƙara yawan kuɗaɗen da take baiwa sojin Amurka a ƙasar ta.
  3. Sudan: Jami'an tsaro sun cafke wasu daga cikin farfesoshin jami'o'i a birnin Khartoum.
  4. Nigeria: Kwanaki uku kafin a yi zaɓen shugaban ƙasa, matasa da suka fito takaran muƙamai sun ce salon mulkin su zai banbanta da na 'yan baya.
    "Almazaranci da kuɗin mutane, da rashin tsaro da ya addabi mutane, da yaudara, da sauransu... da aka saba ganin 'yan siyasa suna yi. Wanda mu ba mu fito ba da wannan..."
  5. Cameroon: Za kuma ku ji kiraye-kirayen da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ke yi wa hukumomin Kamaru domin su sako wata ɗaliba da ake tsare ita.

[50] [51] [52]

23

DW Hausa Shirin Safe (Wed Feb 13th 2019) [53]


Cikin shirin za a ji yadda wasu al'umomi ke bayyana muhimmancin kafar sadarwar rediyo a rayuwarsu ta yau da kullum, dai lokacin da ake ranar rediyo ta duniya. A Najeriya kuwa mazauna yankunan karkara ne ke damuwa da yawan alkawura da 'yan siyasa ke dauka ba tare da cikawa ba.

  1. Host: Munta Gayuwa*
  2. Nigeria: Za mu ji yadda mazauna yankunan karkara a Najeria suke cewa suna cikin halin taƙaici na roman baka da 'yan siyasar ƙasar ke yi musu, tsawon shekaru da ƙasar ta kama mulki irin na demokraɗiya. Toh wane irin alƙauran ne wadannan 'yan siyasa ke yi wa wadannan mutane na karkara?
    "In mun ci zaɓe, za mu yi muku hanya. In mun ci zaɓe, za mu kawo muku wuta, asibiti, da sauran abubuwa. Amma ko ɗaya, ba wanda ya taɓa cika mana. Wani pole-waya an kafa a nan ya kai har shekara goma sha biyu (12), amma wallahi ba a zo yin komai ba!"
  3. Nigeria: Muna tafe da rahoto kan wannan matsala. Hakannan kuma za'a ji al'ummar Fulani da dokar hana kiwo ta shafa a jihar Benue da ke tsakiyar Najeriyar. Sun buƙaci kariya ne daga jami'an tsaro a duk inda suke don basu damar zaɓe kamar sauran 'yan ƙasar Najeriyar.
  4. World Radio Day 2019: Yayin kuma da ake ranar rediyo ta duniya, za mu ji yadda wasu al'ummomi ke bayyana mahimmancin kafarta sadarwa a garesu. (14:44-18:15)[54][55][56]
  5. Morocco: Hukumomi a ƙasar Morocco, sun kama wasu Faransawa da suka ce suna ɗaukar nauyin ƙungiyar nan ta IS.
  6. Nigeria: Mutane da dama sun mutu lokacin gangamin yaƙin neman zaɓe na shugaba Muhammadu Buhari a Najeriya.
  7. Thailand: Wasu fursunoni, wato 'yan ƙabilar Uyghir, sun tsere daga hannun jami'an tsaro a ƙasar Thailand.

[57] [58] [59]

24

DW Hausa Shirin Yamma (Wed Feb 13th 2019) [60]


A cikin shirin za a sha labaran duniya da kuma rahotanni kan zaben Najeriya da rikicin kasar Kamaru na 'yan aware da ke kara kamari. [5]

  1. Hosts: Ramatu Garba Baba, Ahmed Salisu
  2. Nigeria Elections 2019:
    1. 'Yan takara kusan saba'in (nearly 70) suka sanya hannu kan wata sabuwar yarjejeniya, don tabbatar da zaman lafiya a yanzu da ma bayan zab'e.
    2. Jam'iyya da ke mulki (the incumbent party APC) a Najeriyar ta APC kuwa, ta gudanar ko kammala yak'in neman zab'enta a Abuja.
    3. Yayin da ita kuma jam'iyyar adawa ta PDP ta ce a karo na biyu, gwamnati ta hana ta gudanar da nata gangamin. Za mu ji mai hakan ke nufi da demokradiyyan Najeriya.
  3. Mali: Za'a ji yanda k'ungiyoyi na addinin Islama suka k'addamar da gangami don nuna adawa ga halayyar 'yan siyasa.
  4. Venezuela: Shugaba Maduro na Venezuela ya ce dole Juan Guaidó ya gurfana gaban kotu saboda k'eta dokokin k'asa.
  5. Iran: Har kunar bak'in wake ya yi sanadiyyar rasuwar jami'an tsaron Iran ashirin (20).
  6. Nigeria: 'Yan bindiga sun afkawa jerin gwanon motoci na gwamnan jihar Borno.

[61]

25

VOA Hausa Shirin Safe (Thu Feb 14th 2019) [62]


  1. Hosts: Muhammad Hafiz Baballe, Ibrahim Ka-Almasih Garba.
  2. USA, Iran: Amurka tana tuhumar wata tsohuwar jami'ar sojan samanta wadda ta canja sheƙa zuwa ɓangaren Iran da yin mata leƙan asiri.
  3. USA: Shugaban Amurka Donald Trump ya ce har yanzu bai tsaida shawarar rattaba hannu ko a'a kan ƙudurin bai ɗaya da jam'iyyu suka cimma ba wanda ya tanadi kuɗin gina katanga.
  4. USA, Yemen: Majalisar wakilan Amurka mai rinjayin 'yan Democrats, ta kaɗa kuri'ar rage tallafin soji da Amurka ke baiwa gamayyar sojojin da Saudiya ke jagoranta a yaƙin Yemen.
  5. Nigeria Elections 2019: Manyan 'yan takarar shugabancin Najeriya, sun sake jaddada yarjejeniyar zaman lafiya da aka ƙulla.
  6. Nigeria: Gwamnar jihar Borno, Kashim Shettima, ya tsallake rijiya da baya a ƙauyen Lugumanu*.
    "Mu mun ɗauka sojoji ne, ashe ba sojoji ba ne. Suna da kayan sarki kuma dukansu sun more..."
  7. Ba shirin Domin Iyali.

[63] [64] [65]

25

VOA Hausa Shirin Hantsi (Thu Feb 14th 2019) [66]


  1. Hosts: Muhammad Hafiz Baballe, Ibrahim Ka-Almasih Garba.
  2. Nigeria: Ministan tsaron Najeriya, Janar Mansur Dan Ali mai ritaya, ya ƙaryata jita-jita da ake yi na cewa jami'an ƙasar basu da kayan aiki.
    "Ko ƙasar America, ko ƙasar Ingila (England), ko ƙasar Russia, ba za su ce suna da isasshun kaya da suka ishe su ba.
  3. Muƙaddashin shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya, wato EFCC, Ibrahim Mago, ya ce za su gurfanar da masu siyan da ƙuri'a da masu tada fitina lokacin zaɓr a gaban kotu.
  4. Ba shirin Nakasa.
  5. Ghana newspaper headlines <> sharhin jaridun Ghana.
  6. Saƙonnin masu sauraro na kan na'ura.

[67] [68] [69]

26

BBC Hausa Shirin Safe (Thu Feb 14th 2019) [70]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. Nigeria: A Najeriya, an kai wa waɗansu tagwayen hare-hare kan ayarin gwamnan jihar Borno a lokacin yaƙin neman zaɓe a garin Gamboru.
  3. Nigeria Elections 2019: Jam'iyar PDP ta zargi gwamnatin APC da yi mata kwitingila na hana ta yin filin yin taro a Abuja: "Gashi bayan mun yi gangamin mutane, daga ko'ina sun taho, har da masu hawan jakuna da dawakai. Da muka je, muka tarar an sa kwaɗo, an hana." Sai dai kuma, ana ta ɓangaren, APC ta musanta wannan zargin: "Na farko dai, fili na gwamnati ne kuma na tabbata akwai ƙa'idoji wadda ake bi. Maganar cewa wai yau an hana su taro domin wani abu... tsoron faɗuwa ne, shi ya sa suke neman duk ta hanyar da za'a bi a tayar da hankali."
  4. Sudan: BBC ta bankaɗo wani wuri da ake tsare masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnati tare da azabtar da su a ƙasar Sudan.
  5. Taƙaitaccen labarin wasanni.

[71] [72] [73]

27

BBC Hausa Shirin Hantsi (Thu Feb 14th 2019) [74]


  1. Hosts: Badriya Tijjani Kalarawi
  2. Liberia: In gano gawar mutane biyar amma a mahaƙar ma'adinai ta gwal wadda ta rifta a arewacin Liberia a makon da ya wuce.
  3. USA, Yemen: 'Yan majalisar Amurka sun gabatar da uzurin da zai janyowa dakarun ƙasar su janye daga Yemen.
  4. Nigeria Elections 2019: Yayin da ya rage kwanaki biyu a gudanar da zaɓe a Najeriya, masu larura ta musamman na ƙorafi kan jami'an tsaro a rumfunan zaɓe.
    "Dubu biyu da sha biyar (2015), na je zan jefa ƙuri'a na, aka ce min ni in bi layi domin ban fi kowa ba. A bisa ga kundin tsarin dokoki na hukumar zaɓe. Mu akwai kulawa ta musamman. Idan muka zo, ba za mu bi layi ba.
  5. Sports: Real Madrid ta doke Ajax (Ayax) da ci biyu da ɗaya (2-1). Wasan farko, zagaye na biyu a gasar cin kofin zakarin Turai. Sai kuma ana fara yabawa mai horasda Madrid ɗin.

[75] [76] [77]

28

BBC Hausa Shirin Rana (Thu Feb 14th 2019) [78]


  1. Hosts: Sulaiman Ibrahim Katsina
  2. Nigeria Elections 2019:
    1. A yau ne a Najeriya aka shirya soma rarraba kayan aiki don zaɓen shugaban ƙasa da ke tafe ranar Asabar.
    2. Suma masu sa ido, sun buɗe sansaninsu a yau.
    3. Wani kuma, wanda da alama ya fi kowa niyar zaɓen, tun jiya ya isa rumfar zaɓen. Inda yake shirin yin kwanaki uku yana jira kafin a soma kaɗa ƙuri'a.
      "Tun jiya, ƙarfe goma sha ɗaya da rabi (10:30) na bar gida na. Na tattara kayana, na zo na zauna. Zan yi alƙawari kwana uku.
  3. EU: Tarayar Turai ta kammala wani tsari na wata doka, wadda ta shafi haƙƙin mallaka a intanet. Sai dai, akwai masu ƙorafi akan haka. Za mu ji ko su wanene.
  4. Labarin wasanni (sports).

[79] [80] [81]

29

ParsToday Hausa 1 (Thu Feb 14th 2019) [82]


  1. Hosts: Abdullahi Salihu*
  2. Nigeria Elections 2019: Wasu daga cikin jami'an gwamnatin APC a Najeriya sun nuna ɓacin ransu matuƙa dangane da yadda ƙungiyoyi na dattijan arewa da ma wasu daga ɓangaren kudancin ƙasar suka nuna goyan bayansu ga ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyar adawa ta PDP, wato Alhaji Atiku Abubakar.
  3. Ethiopia: Za mu duba yadda masana suke kallon kawo ƙarshen taron shugabannin ƙasashen Afrika, wanda aka gudanar a birnin Adis Ababa na ƙasar Habasha, da kuma abubuwan da taron ya cimmawa game da yiyuwar aiwatar da su a aikace.
  4. France: Za mu duba batun matakan da sojojin gwamnatin ƙasar France suka ɗauka na kare wanda ya juya mulki da suka ce an yi yunƙurin aiwatarwa a ƙasar Cadi.
  5. Iran, Lebanon: Za a ji sharhin [ unintelligible: bayan labaran? ] wadanda suka yi magana akan ziyarar wadansu harkokin wajen Iran a ƙasar Lebanon.
  6. Shirin Ko Kun San, Kaza a kan dame, shirin labaran wasannin mako.
  7. Venezuela: Shugaban ƙasar Venezuela ya ce ƙasar za ta zamai wa Amurka Vietnam matuƙar ta kai mata hari.
  8. Bahrain: An cika shekaru takwas da fara yunƙurin al'umma a ƙasar Bahrain.
  9. China: ƙungiyar kare hakkin bil Adama (human rights) na ƙasashen duniya sun zargi ƙasar China da take hakkokin musulmi.

[83] [84] [85]

Contents